< Psaumes 10 >

1 Pourquoi, Seigneur, t'es-tu retiré au loin; et nous méprises-tu dans l'affliction et au temps du besoin?
Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
2 Pendant que l'impie se gonfle d'orgueil, le pauvre se consume; les méchants seront pris dans les ruses qu'ils avaient conçues.
Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
3 Car le pécheur se loue des désirs de son âme, et l'injuste est comblé de biens.
Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
4 Le pécheur a irrité Dieu; dans la plénitude de sa passion, il n'aura garde de le chercher. Le Seigneur n'est point là devant lui.
Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
5 En tout temps ses voies sont souillées; tes jugements, mon Dieu, sont ôtés de devant sa face; et il prévaudra sur tous ses ennemis.
Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
6 Car il a dit en son cœur: Je ne serai point ébranlé, et de génération en génération je serai sans mal.
Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
7 Sa bouche est pleine de malédiction, d'amertume, de fourberies; la peine et la douleur sont sous sa langue.
Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
8 Il se tient en embuscade avec les riches, dans des lieux cachés, pour tuer l'innocent. Les yeux tournés sur le pauvre,
Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
9 Il l'épie en secret, comme le lion dans son antre; il dresse là ses embûches pour le ravir, après l'avoir attiré.
Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
10 Il le renversera dans ses filets; puis il se baissera et tombera sur lui, quand il se sera rendu maître des pauvres.
Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
11 Car il a dit en son cœur: Dieu a oublié; il a détourné sa face pour ne plus jamais voir.
Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
12 Lève-toi, Seigneur Dieu, lève ta main; n'oublie pas les pauvres!
Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
13 Pourquoi l'impie a-t-il irrité Dieu? Car il a dit en son cœur: Il ne fera pas de recherches.
Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
14 Mais tu vois, tu es attentif à la peine et à la douleur, pour faire tomber dans tes mains les méchants; à toi seul le pauvre est confié, tu es le protecteur de l'orphelin.
Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
15 Broie le bras du méchant et du pécheur; son péché sera recherché, et on ne le trouvera plus.
Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
16 Le Seigneur régnera éternellement dans les siècles des siècles; et vous, Gentils, vous périrez sur la terre qui lui appartient.
Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
17 Le Seigneur a exaucé le désir des pauvres; ton oreille a entendu la préparation de leur cœur.
Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
18 Jugez l'humble et l'orphelin, afin que l'homme sur la terre ne continue pas de s'enorgueillir.
kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.

< Psaumes 10 >