< Psaumes 1 >
1 Heureux l'homme qui n'est point allé au conseil des impies qui ne s'est pas arrêté dans la voie des pécheurs et ne s'est point assis dans la chaire de pestilence,
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 Mais dont la volonté est conforme à la loi du Seigneur, et qui, nuit et jour, méditera sur cette loi.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 Il sera comme l'arbre planté au bord des eaux, et qui donnera son fruit en sa saison; ses feuilles ne tomberont jamais, et en toutes ses œuvres il prospérera.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 Ils ne sont pas ainsi les impies, ils ne sont pas ainsi; mais ils sont comme la paille que le vent balaie sur la face de la terre.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 C'est pourquoi les impies ne ressusciteront pas dans le jugement, ni les pécheurs dans l'assemblée des justes.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 Car le Seigneur connaît la voie des justes; et la voie des pécheurs périra.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.