< Proverbes 8 >
1 Tu proclameras la Sagesse, afin que la prudence t'obéisse.
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Car elle se tient sur les cimes des monts; elle est debout au milieu des sentiers.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Elle s'assied devant les portes des riches, et à l'entrée des villes; elle chante
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 C'est vous, ô hommes, que j'appelle; j'élève ma voix devant les fils des hommes.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Comprenez, innocents, la subtilité; et vous, ignorants, déposez la science en votre cœur.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Écoutez-moi; car je vais dire des choses saintes, et proférer de mes lèvres la justice.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Car ma langue va méditer la vérité, et j'ai en abomination les lèvres menteuses.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Toutes les paroles de ma bouche sont selon la justice; en elles rien d'oblique et de tortueux.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Elles sont toutes offertes à ceux qui comprennent, et justes pour ceux qui trouvent la Sagesse.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Recevez l'instruction et non l'argent, et la science plutôt que l'or raffiné.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Car la sagesse a plus de prix que les pierres précieuses, et rien de ce que l'on estime de plus précieux ne la vaut.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Moi, la Sagesse, j'ai demeuré avec le conseil et le savoir; j'ai appelé à moi l'intelligence.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 La crainte du Seigneur hait l'iniquité, et l'insolence, et l'orgueil et les voies des méchants; et moi aussi, je hais les voies tortueuses des méchants.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 C'est à moi le conseil et la fermeté, à moi la prudence, à moi la force.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Par moi, les rois règnent, et les princes écrivent des jugements équitables.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Par moi, les grands sont glorifiés; par moi, les monarques commandent à la terre.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Moi j'aime ceux qui m'aiment, et ceux qui me cherchent me trouvent.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 De moi dépendent la fortune et la gloire, et les grandes richesses et la justice.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Mieux vaut recueillir mes fruits que de l'or et des pierres précieuses, et mes rejetons sont meilleurs que l'argent le plus pur.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Je me promène dans les voies de l'équité, et je reviens par les voies de la justice;
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 pour distribuer à ceux qui m'aiment une part de mes richesses, et remplir de biens leurs trésors. Après vous avoir publié ce qui arrive chaque jour, je vais énumérer les choses qui sont de toute éternité.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Le Seigneur m'a créé au commencement de Ses voies, pour faire Ses œuvres.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Il m'a établie avant le temps, au commencement, avant de créer la terre,
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 et avant de créer les abîmes, avant que l'eau jaillit des fontaines.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Il m'a engendrée avant que les montagnes et les collines fussent affermies.
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Le Seigneur a fait les champs et les déserts, et les cimes habitées sous le ciel.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Quand Il a préparé le ciel, j'étais auprès de Lui, et lorsqu'Il a élevé Son trône sur les vents,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 et lorsqu'en haut Il a donné aux nuées leur cohérence, et aux fontaines qui sont sous le ciel leur équilibre,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 et lorsqu'Il a affermi les fondements de la terre;
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 j'étais là, près de Lui, disposant tout avec Lui; j'étais là, et Il Se délectait en moi; chaque jour, à tout moment, je me réjouissais de la vue de Son visage;
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 lorsqu'Il S'applaudissait d'avoir achevé la terre, et Se complaisait dans les fils des hommes.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Maintenant donc, mon fils, écoute-moi:
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Heureux l'homme qui m'écoutera, et le mortel qui gardera mes voies, veillant le jour à mes portes et gardant le seuil de ma demeure.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Car mes portes sont des portes de vie, et en elles réside la volonté du Seigneur.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Ceux qui pèchent contre moi outragent leur âme, et ceux qui me haïssent aiment la mort.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”