< Proverbes 20 >
1 Le vin est déréglé, et l'ivresse insolente; l'insensé se laisse prendre dans leurs filets;
Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
2 La menace d'un roi ne diffère point de la colère du lion; celui qui le provoque pèche contre sa propre vie.
Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
3 C'est une gloire pour un homme de se détourner des contestations; au contraire, le fou s'y laisse prendre.
Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
4 Le paresseux, quand on le blâme, n'en a point honte; il en est de même de celui qui emprunte du blé à usure pendant la moisson.
Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
5 Le conseil dans le cœur de l'homme est une eau profonde; l'homme prudent y saura puiser.
Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
6 Un homme est une grande chose; un homme miséricordieux est un trésor; mais un homme fidèle est difficile à trouver.
Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
7 L'homme irréprochable qui se tourne vers la justice laissera ses enfants heureux.
Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
8 Lorsqu'un roi juste s'est assis sur son trône, nul mal ne résiste à ses regards.
Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
9 Qui peut se vanter d'avoir le cœur chaste? Qui osera dire: Je suis pur de tout péché?
Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
10 Avoir deux poids et deux mesures, et en faire usage: deux choses infâmes devant le Seigneur.
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
11 Le jeune homme en compagnie d'un saint sera réservé dans ses mœurs, et sa voie sera droite.
Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
12 L'oreille entend, et l'œil voit; l'un et l'autre sont l'œuvre du Seigneur.
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
13 Ne te plais pas à médire, si tu ne veux être chassé. Ouvre les yeux, et rassasie-toi de pain.
Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
“Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
20 La lampe de celui qui décrie son père ou sa mère s'éteindra; les prunelles de ses yeux verront les ténèbres.
In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
21 Le bien acquis tout d'abord à la hâte, à la fin ne sera pas béni.
Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
22 Garde-toi de dire: Je me vengerai de mon ennemi; mais attends le Seigneur, afin qu'Il te seconde.
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
23 Le double poids est en abomination au Seigneur, et les fausses balances ne sont point bonnes à Ses yeux.
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
24 La marche d'un homme est maintenue droite par le Seigneur; car comment un mortel discernerait-il ses voies?
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
25 L'homme tombe dans un piège, quand il se hâte trop de consacrer ses biens; car après le vœu vient le repentir.
Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
26 Un roi sage est le vanneur des impies, et il fait passer sur eux une roue.
Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
27 L'esprit de l'homme est une lumière du Seigneur, qui éclaire jusqu'au fonds des entrailles.
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
28 La miséricorde et la vérité sont la garde du roi, et avec la justice elles font cercle autour de son trône.
Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
29 L'ornement des jeunes gens c'est la sagesse; la parure des vieillards, ce sont leurs cheveux qui grisonnent.
Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
30 Les confusions et les blessures sont le partage des méchants; ils ont des plaies jusqu'au fond des entrailles.
Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.