< Nombres 34 >
1 Et le Seigneur parla à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Donne mes ordres aux fils d'Israël, et dis-leur: Vous allez entrer en la terre de Chanaan; cette terre, avec ses limites, vous appartiendra comme héritage.
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 Au midi, vous la possèderez depuis le désert jusqu'au territoire d'Edom; de ce côté, la limite sera d'abord le rivage oriental de la mer Salée.
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 Vos limites au midi tourneront autour de la montée d'Acrabin; elles traverseront Ennac (Senna), et elles descendront au delà de Cadès-Barné; puis, elles sortiront du village d'Arad, et elles passeront par Asémona.
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 A partir d'Asémona, elles suivront les contours du torrent d'Egypte, et finiront à la mer.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 Ensuite, vous aurez pour limites la mer, la grande mer vous limitera; ce sera la frontière occidentale.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 Au nord, voici quelle sera votre limite: à partir de la mer, vous mesurerez pour vous la montagne, le long de la montagne.
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 Et vous mesurerez pour vous de montagne en montagne; votre frontière, après être entrée dans Emath, ira jusqu'à Saradac (Sadada).
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 Ensuite, elle sortira de Déphron (Zéphronie), et finira en Arsenaïn (Enan): telle sera votre frontière du nord.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 Et tous mesurerez votre frontière orientale d'Arsenaïn à Séphama;
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 Elle descendra de Séphama en Béla (Rébla), au delà des frontières, et de Béla à l'extrémité de la rive orientale de la mer de Cénéreth (Génésareth).
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 Puis, elle suivra le cours du Jourdain, et elle finira par la mer Salée: telle sera votre terre, telles seront ses limites tout alentour.
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Moïse donna donc cet ordre aux fils d'Israël, disant: Voici la terre que vous vous partagerez au sort, comme l'a prescrit le Seigneur, pour la distribuer aux neuf tribus et à la demi-tribu de Manassé.
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 Car les fils de Ruben, les fils de Gad, par familles paternelles, et une demi-tribu de Manassé, ont reçu leurs parts.
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 Deux tribus et une demi-tribu ont pris leur part, vis-à-vis Jéricho, sur la rive orientale du Jourdain, au sud-est
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 Et le Seigneur parla à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Voici les noms des hommes qui procèderont au partage de la terre: Eléazar le prêtre, et Josué, fils de Nau.
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 Et vous prendrez par tribu un prince qui tirera au sort la part de la tribu.
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 Voici les noms de ces princes, pour la tribu de Juda: Caleb, fils de Jéphoné.
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 Pour la tribu de Siméon: Samuel, fils d'Ammiud.
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 Pour la tribu de Benjamin: Elidad, fils de Chaselon.
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 Pour la tribu de Dan: Bocchi, fils de Jogli.
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 Pour les fils de Joseph, de la tribu de Manassé: Hanniel, fils d'Ephod;
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 Pour la tribu d'Ephraïm: Camuel, fils de Sephthan;
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 Pour la tribu de Zabulon: Elisaphan, fils de Pharnach.
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 Pour la tribu d'Issachar: Phaltiel, fils d'Ozan.
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 Pour la tribu d'Aser: Ahiud, fils de Salomi.
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 Et pour la tribu de Nephthali: Phédaël, fils d'Ammiudi
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 Tels furent ceux à qui le Seigneur ordonna de faire les parts des fils d'Israël, en la terre de Chanaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.