< Néhémie 8 >

1 Et le septième mois arriva, et les fils d'Israël étaient dans leurs villes; et tout le peuple se rassembla, comme un seul homme, sur la place, devant la porte de l'Eau; et ils dirent à Esdras le scribe d'apporter le livre de la loi de Moïse que le Seigneur a intimée à Israël.
sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
2 Et le premier jour du septième mois, Esdras, le prêtre, apporta la loi devant la multitude d'hommes et de femmes, et devant tous ceux qui pouvaient l'entendre.
Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
3 Et il la lut depuis l'heure où le soleil éclaire jusqu'au milieu du jour, devant les hommes et les femmes, et ils la comprenaient, et les oreilles de tout le peuple étaient attentives au livre de la loi.
Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
4 Et Esdras, le scribe, se tenait sur une estrade de bois, et il y avait auprès de lui, à sa droite: Matthathias, Samaïas, Ananias, Urie, Helcias et Maasia; à sa gauche: Phadaïas, Misahel, Melchias, Asom, Asubadma, Zacharie et Mesollam.
Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
5 Et Esdras ouvrit le livre à la vue de tout le peuple, car lui-même était plus élevé que le peuple, et lorsqu'il ouvrit le livre, tout le peuple resta debout.
Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
6 Et Esdras bénit le Seigneur, le Dieu très-grand, et le peuple élevant les mains, répondit: Amen. Et ils s'inclinèrent, et ils adorèrent le Seigneur la face contre terre.
Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
7 Ensuite, Josué, Banaïas et Sarabias, expliquèrent la loi au peuple, et le peuple ne bougea pas de sa place.
Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
8 Et ils lurent dans le livre de la loi de Dieu; puis, Esdras enseigna, et il apprit au peuple à connaître le Seigneur, et le peuple comprit à la lecture.
Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
9 Alors, Néhémias et Esdras, le scribe et prêtre, et les lévites qui expliquaient la loi au peuple, dirent à tout le peuple: Ce jour est consacré au Seigneur notre Dieu, ne vous affligez pas, ne pleurez point. Car tout le peuple pleurait quand il entendait les paroles de la loi.
Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
10 Et Néhémias leur dit: Allez, mangez des chairs grasses, buvez de douces boissons, et envoyez des parts à ceux qui n'en ont point, car ce jour est consacré au Seigneur notre Dieu, et ne soyez point abattus, puisque le Seigneur est notre force.
Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
11 Et les lévites faisaient taire tout le peuple, disant: Gardez le silence, car ce jour est saint, et ne soyez point abattus.
Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
12 Et tout le peuple s'en alla pour manger, boire, envoyer des parts et faire grande liesse, parce qu'il avait compris les paroles que Néhémias leur avait fait connaître.
Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
13 Et le second jour, les chefs de famille, tout le peuple, les prêtres et les lévites, se réunirent autour d'Esdras, le scribe, pour qu'il les instruisît sur toutes les paroles de la loi.
A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
14 Et ils trouvèrent écrit en la loi que le Seigneur avait commandé à Moïse que les fils d'Israël demeurassent sous des tabernacles, durant la fête du septième mois,
Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
15 Et qu'ils le publiassent au son de la trompette en toutes leurs villes et à Jérusalem. Et Esdras dit: Allez sur la montagne, rapportez-en des rameaux d'olivier, de cyprès, de tamaris, de palmier et de tous les arbres touffus, pour faire des tabernacles selon ce qui est écrit.
kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
16 Et le peuple sortit, et il rapporta des rameaux, et ils se firent des tabernacles, chacun sur sa terrasse, ou dans sa cour, ou dans les parvis du temple du Seigneur, ou dans les rues de la ville jusqu'à la porte d'Ephraïm.
Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
17 Et toute l'Église, tous ceux qui étaient revenus de la captivité se firent des tabernacles, et ils demeurèrent sous des tabernacles; et depuis le temps de Josué, fils de Nau, jusqu'à ce jour-là, le peuple d'Israël n'avait pas fait ainsi, et grande fut sa joie.
Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
18 Et on lut dans le livre de la loi, tous les jours, depuis le premier jusqu'au dernier, et ils firent la fête sept jours, et le huitième jour la fin de la fête, selon la loi.
Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.

< Néhémie 8 >