< Michée 7 >
1 Malheur à moi! me voilà comme celui qui ramasse du chaume en la moisson, ou qui cueille un grappillon de la vendange, n'ayant pas à lui une seule grappe pour en manger les prémices; malheur à mon âme!
Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
2 Car le juste a péri sur la terre; et parmi les hommes il n'en est pas qui marche droit. Tous sont en justice pour avoir versé le sang; et chacun d'eux accable son prochain sous l'oppression.
An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
3 Et leurs mains sont prêtes à faire le mal. le prince exige; le juge dit des paroles douces; et voici le désir de son âme: Je prendrai leurs biens,
Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
4 comme le ver qui ronge, marchant décemment au jour de la visite. Malheur! Tes vengeances, Seigneur, sont venues, et maintenant vont venir leurs lamentations.
Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
5 Ne vous fiez pas à vos amis, n'espérez pas en vos princes; garde-toi même de ton épouse, et ne lui confie quoi que ce soit.
Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
6 Car le fils outragera le père; la fille se révoltera contre sa mère, la bru contre sa belle-mère; l'homme aura pour ennemis tous ceux de sa maison.
Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
7 Pour moi, je regarderai le Seigneur; j'attendrai le Dieu mon Sauveur, et mon Dieu m'exaucera.
Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
8 Ne m'insulte pas, ô mon ennemie, parce que je suis tombée, je me relèverai; car, si je suis à terre dans les ténèbres, le Seigneur m'éclairera.
Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
9 Parce que j'ai péché contre le Seigneur, je supporterai Sa colère jusqu'à ce qu'Il ait reconnu juste ma cause. Et alors Il me rendra justice, et Il me ramènera à la lumière, et je verrai Son équité.
Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
10 Et mon ennemie verra cela; et elle sera couverte de honte, celle qui dit maintenant: Où est le Seigneur ton Dieu? Mes yeux la regarderont alors, et elle sera foulée aux pieds comme la boue des rues.
Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
11 Voici le jour où l'on enduit la brique; ce jour sera celui de ta destruction, et ce jour-là tes lois seront effacées,
Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
12 et tes villes seront mises au niveau du sol; elles seront partagées entre les Assyriens; et tes forteresses seront partagées, depuis Tyr jusqu'au fleuve, d'une mer à l'autre, et d'une montagne à l'autre.
A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
13 Et ta terre et tous ceux qui l'habitent seront désolés, à cause des fruits de leur convoitise.
Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
14 Ta verge à la main, Seigneur, pais les brebis de Ton héritage, qui d'elles-mêmes se sont abritées dans la forêt du Carmel. Elles trouveront leur pâture en Basan et Galaad, comme aux jours d'autrefois,
Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
15 comme aux jours où Tu nous as fait sortir d'Égypte. Vous verrez des prodiges;
“Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
16 et les gentils les verront aussi, et ils en seront confondus malgré toute leur puissance, ils se mettront la main sur la bouche, et leurs oreilles n'entendront plus.
Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
17 Ils lécheront la terre comme les serpents qui rampent dans la poussière; ils seront pleins de trouble dans l'enceinte de leurs remparts; ils seront hors d'eux-mêmes, à cause du Seigneur notre Dieu, et ils auront peu de Lui.
Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
18 Qui donc est Dieu comme Toi, qui ôtes les péchés, et passes sous silence les impiétés de ce qui reste de Ton héritage! Le Seigneur n'a point maintenu le témoignage de Sa colère; Il Se complaît en Sa miséricorde;
Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
19 Il reviendra; Il aura compassion de nous; Il submergera nos iniquités; Il jettera nos péchés au fond de la mer.
Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
20 Il fera des dons à Jacob, en vérité; Il sera miséricordieux envers Abraham, comme Il l'a juré à nos pères aux jours d'autrefois.
Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.