< Lamentations 3 >

1 Aleph. Je suis l'homme qui voit sa misère, parce que la verge de la colère du Seigneur est sur moi.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Il m'a saisi et il m'a conduit dans les ténèbres, et non à la lumière.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Il n'a fait que tourner la main sur moi, durant tout le jour.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Il a envieilli ma peau et ma chair; il a brisé mes os.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Beth. Il a bâti contre moi; il a entouré ma tête; il a travaillé à ma perte;
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 Il m'a mis dans les ténèbres, comme les morts des siècles passés.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Il a bâti contre moi, et je ne sortirai plus; il a appesanti mes fers.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Ghimel. Et quand je crierais, quand je l'invoquerais, c'est en vain; il a clos ma prière.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Daleth. Il a muré mes voies; il a barricadé mes sentiers; il les a confondus.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Il est pour moi une ourse qui me guette, un lion dans son repaire.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Il m'a poursuivi, comme je me détournais; il m'a arrêté, il m'a effacé;
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Hé. Il a tendu son arc; il m'a fait tenir comme un but de flèches.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Il a plongé dans mes reins les traits de son carquois.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Je suis devenu la risée de tout mon peuple, le sujet de leurs chants, pendant tout le jour.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Vav. Il m'a nourri d'amertume; il m'a enivré de fiel.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Il m'a brisé les dents avec des cailloux; il m'a donné à manger de la cendre.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Il a banni la paix de mon âme; j'ai oublié toutes mes joies:
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Mes biens ont péri; mais mon espérance est dans le Seigneur.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Zaïn. Je me suis souvenu de ma misère; et, persécuté comme je suis, mon amertume et mon fiel
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Ne seront pas oubliés; et les méditations de mon âme se tourneront contre moi.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Je les enfermerai dans mon cœur, et à cause de cela je souffrirai avec patience.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Teth. Le Seigneur est bon pour ceux qui l'attendent. C'est un bien pour l'âme de le chercher;
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Teth. Le Seigneur est bon pour ceux qui l'attendent. C'est un bien pour l'âme de le chercher;
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Teth. Le Seigneur est bon pour ceux qui l'attendent. C'est un bien pour l'âme de le chercher;
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Teth. Le Seigneur est bon pour ceux qui l'attendent. C'est un bien pour l'âme de le chercher;
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Elle patientera, elle attendra paisiblement le salut du Seigneur.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Il est bon à l'homme d'être soumis au joug dès sa jeunesse.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Il se tiendra solitaire; et il se taira, parce qu'il l'aura porté sur lui.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Iod. Il tendra la joue à qui le frappe; il se rassasiera d'opprobre,
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Iod. Il tendra la joue à qui le frappe; il se rassasiera d'opprobre,
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Parce que le Seigneur ne répudie pas pour toujours.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Coph. Si c'est lui qui a humilié, il aura compassion dans la plénitude de sa miséricorde.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Car ces paroles de colère ne sont pas selon son cœur, et ceux qu'il a abaissés sont des fils de l'homme.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Lamed. Mettre sous ses pieds tous les captifs de la terre,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 Refuser justice à un homme devant le Très-Haut,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 Condamner un homme quand on doit le juger, le Seigneur ne l'a pas dit.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Qui est celui qui a dit de telles choses, et a été obéi? Ce n'est pas le Seigneur qui les a commandées.
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Le mal ne sortira pas de la bouche du Seigneur en même temps que le bien.
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Mem. Pourquoi murmure-t-il, l'homme vivant, l'homme qui songe à son péché?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Noun. Votre voie a été examinée et recherchée, retournez au Seigneur.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Élevons nos cœurs sur nos mains, vers le Très-Haut, dans le ciel.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 Nous avons péché, nous avons été impies, et vous ne nous avez point pardonné.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Samech. Vous avez gardé votre ressentiment, et vous nous avez poursuivis; vous avez tué, et vous n'avez rien épargné.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Vous vous êtes voilé d'une nuée pendant ma prière, pour ne plus me voir
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Et pour me répudier; Aïn. Vous nous avez isolées au milieu des peuples.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Tous nos ennemis ont ouvert la bouche contre nous.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 La crainte et la fureur, l'orgueil et la ruine sont venus en nous.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Mon œil répandra des torrents de larmes sur la destruction de la fille de mon peuple.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Phé. Mon œil s'est consumé; et je ne me tairai point, parce qu'il n'y aura point de repos pour moi
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Avant que le Seigneur, du haut des cieux, se penche et regarde.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mon œil ravagera mon âme, à la vue de toutes les filles de la cité.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Tsadé. Des oiseleurs m'ont fait la chasse comme à un passereau; ce sont tous ceux qui me haïssent sans raison.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Ils m'ont jeté dans une citerne pour m'ôter la vie, et ils en ont posé le couvercle sur moi.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 L'eau s'est répandue sur ma tête, et j'ai dit: Je suis perdu.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Coph. J'ai invoqué votre nom, ô Seigneur, du fond de la citerne;
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Vous avez entendu ma voix, et vous n'avez point fermé les oreilles à ma prière.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Vous êtes venu à mon secours le jour où je vous avais invoqué, et vous m'avez dit: Ne crains pas.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Resch. Seigneur, vous avez plaidé la cause de mon âme; vous avez racheté ma vie.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Seigneur, vous avez vu mes troubles; vous m'avez rendu justice.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Vous avez vu toute leur vengeance, tous leurs desseins sur moi.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Schin. Vous avez entendu leurs outrages, et tous leurs desseins contre moi,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 Et les lèvres de mes oppresseurs, et leurs complots tramés contre moi tout le jour.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Soit qu'ils s'asseyent, soit qu'ils se lèvent, considérez leurs yeux.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Seigneur, vous les rétribuerez selon les œuvres de leurs mains.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Thav. Vous leur ferez expier votre protection et les peines de mon cœur.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Vous les poursuivrez en votre colère, et vous les ferez disparaître de dessous le ciel, ô Seigneur.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >