< Josué 23 >

1 Et bien des jours s'étaient écoulés après que le Seigneur avait donné le repos à Israël; les ennemis qui l'entouraient étaient désarmés. Josué était vieux, et avait vécu bien des jours.
An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
2 Et Josué convoqua tous les fils d'Israël, leurs anciens, leurs chefs, leurs juges, leurs scribes, et il leur dit: Je suis vieux, j'ai vécu bien des jours,
sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
3 Et vous avez vu comment le Seigneur notre Dieu a traité toutes ces nations devant vous, parce que le Seigneur lui-même a combattu pour vous.
ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
4 Vous voyez que je vous ai soumis ce qui reste de toutes ces nations parmi vous, sur les territoires de vos tribus; je les ai exterminées entre le Jourdain et la grande mer qui sera votre limite à l'occident.
Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
5 Le Seigneur votre Dieu lui-même continuera de les exterminer devant vous, jusqu'à ce qu'elles soient toutes détruites; il enverra contre elles des bêtes farouches, tant qu'il ne les aura pas exterminées devant vous, elles et leurs rois; vous hériterez de leurs terres, comme l'a dit le Seigneur notre Dieu.
Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
6 Efforcez-vous donc avec zèle de garder et de pratiquer tout ce qui est écrit au livre de la loi de Moïse, afin de ne vous en écarter ni à droite ni à gauche;
“Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
7 Afin de ne vous point mêler à ces nations qui existent encore. Que le nom de leurs dieux ne soit jamais prononcé parmi vous; gardez-vous de les servir ou de les adorer.
Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
8 Mais restez fortement attachés au Seigneur notre Dieu, comme vous l'avez été jusqu'à ce jour.
Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
9 Et le Seigneur exterminera, devant votre face, ces nations grandes et puissantes; nulle, jusqu'à ce jour, n'a tenu devant vous.
“Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
10 Un seul de vous a mis en fuite mille hommes, parce que le Seigneur notre Dieu lui-même a combattu pour vous, comme il vous l'a dit.
Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
11 Et vous veillerez diligemment à aimer le Seigneur votre Dieu.
Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
12 Car, si vous vous détournez de lui, si vous vous joignez aux nations qui sont restées parmi vous, si vous contractez chez elles des mariages, si vous vous mêlez à elles et elles à vous,
“Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
13 Vous reconnaîtrez que le Seigneur ne continuera plus d'exterminer ces nations devant votre face. Et pour vous, elles seront des filets, des pièges, des clous sous vos pieds, et des flèches dans vos yeux, jusqu'à ce que vous soyez effacés de cette terre fortunée que vous a donnée le Seigneur notre Dieu.
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
14 Pour moi, je m'en vais à grands pas sur le chemin de la vie, comme font ceux qui sont sur la terre. Et vous, vous reconnaîtrez, en vos cœurs et en vos âmes, que nulle parole n'est tombée à terre de toutes celles qu'a prononcées le Seigneur notre Dieu sur tout ce qui vous concernait, et qu'il n'en a laissé aucune en arrière.
“Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
15 Or, de même que toutes les bonnes paroles du Seigneur se sont accomplies pour vous, de même le Seigneur sera fidèle à toutes ses menaces, jusqu'à ce qu'il vous ait effacés de cette terre fortunée que vous a donnée le Seigneur,
Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
16 Si vous violez l'alliance du Seigneur notre Dieu que lui-même vous a donnée pour loi, si vous vous en allez servir d'autres dieux et les adorer.
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”

< Josué 23 >