< Josué 17 >

1 L'héritage de la tribu des fils de Manassé, premier-né de Joseph, fut donné dans les pays de Galaad et de Basan, d'abord à Machir, premier-né de Manassé, père de Galaad, car c'était un guerrier vaillant,
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 Puis, au reste des fils de Manassé par familles, aux fils de Jézi, aux fils de Célez, aux fils de Jéziel, aux fils de Sichem, aux fils de Symarim et aux fils d'Opher: tels étaient les chefs mâles des familles.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 Or, à Salphaad, fils d'Opher, il n'était point né de fils, mais des filles; et voici les noms des filles de Salphaad: Maala, Nova, Egla, Melcha et Thersa;
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 Elles comparurent devant Eléazar le prêtre, devant Josué et devant les princes, disant: Notre Dieu a commandé par la voix de Moïse qu'il nous fut donné un héritage, au milieu de nos frères; selon l'ordre du Seigneur, on leur donna donc un héritage parmi les frères de leurs pères.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 Les terres qu'on leur distribua étaient du côté d'Anassa et de la plaine de Labec, dans la contrée de Galaad, qui est au delà du Jourdain.
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 Parce que les filles des fils de Manassé devaient avoir leur part, au milieu de leurs frères, et que la contrée de Galaad appartenait aux fils de Manassé qui étaient restés de l'autre côté du fleuve.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 La limite des fils de Manassé commence à Délanath, lieu situé vis-à-vis les fils d'Anath; puis, elle s'avance vers Jamin, vers Jassib et vers la fontaine de Taphthoth.
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 Tout cela appartient aux fils de Manassé, et Tapheth, sur les limites de Manassé, est aux fils d'Ephraïm.
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 Ensuite, la limite descend, du côté du midi, vers le val de Carana, le long du val de Jariel-Téréminthe, qui appartient à Ephraïm, au milieu des villes de Manassé, et la limite de Manassé du côté du nord entre dans le torrent, et elle aboutit à la mer.
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 La rive méridionale du torrent appartient à Ephraïm, et la rive septentrionale à Manassé; la mer est la limite de ces derniers; au nord, ils atteignent Aser, et Issachar du côté du levant.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 Manassé pénètre dans Issachar et dans Aser; il leur prend Bethsan et ses villages, les habitants de Dor et les villages de cette ville, les habitants de Mageddo et les villages de cette ville, enfin, le tiers de Mapheta et les villages de cette ville.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 Les fils de Manassé n'ont pu détruire ces villes. Et le Chananéen continua d'habiter la contrée.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 Lorsque les fils d'Israël, devenus plus puissants, eurent assujetti les Chananéens, quoiqu'ils fussent maîtres de les exterminer, ils les épargnèrent.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 Or, les fils de Joseph parlèrent à Josué, disant: Pourquoi ne nous as-tu donné qu'une part, qu'un seul héritage? Je suis un peuple nombreux, et le Seigneur m'a béni.
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 Et Josué leur dit: Tu es un peuple nombreux, monte dans la forêt et défriche-la pour toi, si tu es trop à l'étroit sur les montagnes d'Ephraïm.
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 Et ils dirent: Les montagnes d'Ephraïm ne nous plaisent point, car le Chananéen qui y demeure à Bethsan et ses villages, dans la vallée de Jesraël, a une cavalerie d'élite et du fer.
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 Et Josué dit aux fils de Joseph: Puisque tu es un peuple nombreux et que tu as une grande puissance, tu ne le borneras pas à un seul héritage;
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 La forêt t'appartiendra; car il y a là une forêt, tu la défricheras; elle sera à toi, lorsque tu auras exterminé le Chananéen; quoiqu'il ait une cavalerie d'élite, tu es plus fort que lui.
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”

< Josué 17 >