< Joël 2 >

1 Sonnez de la trompette du haut de Sion, publiez à grands cris sur la montagne sainte; et que tous ceux qui habitent la terre soient confondus, parce que voilà le jour du Seigneur; il est près de vous,
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 ce jour d'obscurité et de ténèbres, ce jour de nuées et de brouillards. Un peuple nombreux et puissant va se répandre sur les montagnes, comme la lumière du matin; jamais, dans les temps passés, on n'a vu son pareil, et après lui on n'en verra point de semblable durant les années, de générations en générations.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 Ce qui marche devant lui est un feu dévorant; ce qui marche à sa suite est une flamme ardente. La terre, avant qu'il arrive, était comme un jardin de délices; quand il fut passé, c'était un champ désert, et nul ne lui échappera.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 Ils apparaîtront comme une vision de chevaux; ils courront comme des cavaliers.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 Ils s'élanceront sur les cimes des montagnes, comme un bruit de chars, comme un bruit de flammes dévorant des maisons, comme un peuple puissant et nombreux se rangeant en bataille.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Devant leur force, les peuples seront broyés; tout visage sera comme le côté brûlé d'une chaudière.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 Ils courront comme des combattants; ils escaladeront les murailles comme des hommes de guerre; et chacun d'eux marchera dans sa voie, et ils ne dévieront pas de leurs sentiers;
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 et nul ne s'écartera de son frère; ils marcheront chargés de leurs armes; ils tomberont avec leurs traits, et ils ne seront pas détruits.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 Ils prendront la ville; ils courront sur les remparts; ils monteront sur les maisons; ils entreront comme des larrons par les fenêtres.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 Devant leur face, la terre sera confondue, et le ciel tremblera. le soleil et la lune seront voilés de ténèbres, et les étoiles retireront leur lumière.
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 Et le Seigneur fera entendre Sa voix devant Son armée, car Son camp est très nombreux, et les œuvres qui accomplissent Ses paroles sont puissantes, et le jour du Seigneur est un grand jour: il est éclatant; et qui sera capable de le soutenir?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 Et maintenant le Seigneur Dieu vous dit: Convertissez-vous à Moi de toute votreâme; jeûnez, pleurez, frappez-vous la poitrine.
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 Déchirez vos cœurs, et non vos vêtements. Et convertissez-vous au Seigneur votre Dieu, parce qu'Il est plein de clémence et de compassion, patient, abondant en miséricorde, et repentant des maux qu'Il fait en punissant.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Qui sait s'Il ne Se repentira pas, s'Il ne laissera pas après Lui des bénédictions, des offrandes et des libations pour le Seigneur votre Dieu.
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Sonnez de la trompette en Sion; sanctifiez le jeûne; publiez le service de Dieu;
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 réunissez le peuple; sanctifiez l'Église; rassemblez les anciens; rassemblez les enfants à la mamelle; que l'époux quitte sa couche, et la femme son lit nuptial.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Que les prêtres qui servent le Seigneur pleurent au pied de l'autel; qu'ils disent: Seigneur, épargne Ton peuple; ne livre pas Ton héritage à l'opprobre; ne laisse pas les gentils dominer sur lui, de peur que l'on ne dise parmi les nations: Où est leur Dieu?
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 Mais le Seigneur a été jaloux de Sa terre, et Il a épargné Son peuple.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 Et le Seigneur a parlé, et Il a dit à Son peuple: Voilà que Je vous enverrai du blé, du vin et de l'huile, et vous vous en rassasierez, et Je ne vous livrerai pas plus longtemps aux opprobres des gentils.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 Et Je chasserai loin de vous celui qui est venu de l'aquilon; Je le repousserai dans une contrée aride, et Je ferai disparaître sa tête dans la première mer, et sa queue dans la dernière; et sa pourriture montera, et son infection s'élèvera; car il s'est glorifié de ses œuvres.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Rassure-toi, terre; réjouis-toi et tressaille d'allégresse, parce que le Seigneur se glorifie d'agir.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Rassurez-vous, bêtes des champs, les plaines du désert ont bourgeonné; les arbres ont porté leurs fruits; le figuier et la vigne ont donné toute leur force.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 Et vous, enfants de Sion, réjouissez-vous, tressaillez d'allégresse dans le Seigneur votre Dieu; Il vous a donné abondance de vivres; Il fera pleuvoir pour vous, comme autrefois, les pluies du printemps et de l'automne.
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 Et vos granges seront remplies de blé; et vos pressoirs regorgeront de vin et d'huile.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 Et Je vous dédommagerai des ravages que pendant des années ont faits la sauterelle et la grande sauterelle, la nielle et la chenille, Ma grande armée que J'ai envoyée contre vous.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 Et vous mangerez, et vous serez rassasiés, et vous louerez le Nom du Seigneur votre Dieu, à cause des prodiges qu'en votre faveur Il aura faits. Et Mon peuple ne sera plus humilié.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 Et vous connaîtrez que Je suis au milieu d'Israël, et que Je suis le Seigneur votre Dieu, et qu'il n'est point d'autre Dieu que Moi, et Mon peuple ne sera plus humilié à jamais.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 Et ensuite, voici ce qui arrivera: Je répandrai Mon Esprit sur toute chair; et vos fils prophétiseront, et vos anciens auront des songes, et vos jeunes hommes des visions.
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 Et en ce jour-là Je répandrai Mon Esprit sur Mes serviteurs et sur Mes servantes.
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 Et Je mettrai des signes au ciel; et sur la terre, du sang, du feu et de la fumée.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 Le soleil sera changé en ténèbres, et la lune en sang, avant qu'arrive le grand jour, le jour éclatant du Seigneur.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 Et il arrivera que quiconque invoquera le Nom du Seigneur sera sauvé; car alors sera sauvé tout ce qui sera sur la montagne de Sion et de Jérusalem, et avec eux tous les évangélisés que le Seigneur a élus, comme l'a dit le Seigneur.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.

< Joël 2 >