< Job 8 >

1 Et Baldad de Sauchée répondant dit:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Jusqu'à quand parleras-tu de la sorte? Quel esprit verbeux s'exprime par ta bouche?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Dieu est-il un juge prévaricateur? Le créateur de toutes choses torture-t- il l'équité?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 Si tes fils ont péché devant lui, il leur a, de sa main, fait expier leurs fautes.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 Commence donc dès l'aurore à prier le Seigneur tout-puissant.
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 Si tu es pur et sincère, il t'exaucera et il te traitera selon sa justice.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 Ce que tu possédais d'abord te semblera médiocre; ce que tu posséderas finalement sera inexprimable.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 Remonte jusqu'à la première génération; suit à la trace les générations de nos pères.
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 Car nous sommes d'hier et nous ne savons rien; notre vie sur la terre est une ombre.
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 N'est-ce donc pas à nos pères de t'instruire, de t'éclairer, et de tirer de leur cœur les paroles que je vais dire?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Le papyrus croît-il sans eau? L'herbe des prairies pousse-t-elle si elle n'est pas arrosée?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 La fauche-t-on quand elle est encore près de la racine? Et la plante que rien n'abreuve ne dessèche-t-elle pas?
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Ainsi finissent ceux que le Seigneur oublie, car l'espérance de l'impie est vaine.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 Sa maison sera déserte; sa tente disparaîtra comme une toile d'araignée.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 Il aura beau l'étayer, elle ne sera pas solide; dès qu'il en sera enlevé, elle s'écroulera.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 Il y a de l'humidité sous le soleil, une tige sort de la moisissure qu'elle engendre.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 Elle s'élève sur un tas de pierres; elle subsiste au milieu des cailloux.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 Et s'ils viennent à la dévorer, le lieu même se prêtera à nier son existence. N'as-tu pas vu pareille chose?
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 N'est-ce pas comme cette tige que succombe l'impie? Une autre plante hors de terre germera.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Jamais le Seigneur ne rejettera l'innocence; il n'acceptera pas les dons des pervers.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 Il mettra le sourire sur les lèvres des hommes sincères, et leur bouche sera pleine de ses louanges.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Leurs ennemis seront couverts de honte; et il n'y aura pas de vie heureuse pour les méchants.
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Job 8 >