< Job 6 >
2 Plût à Dieu que l'on mît à la fois dans une balance ma colère et mes douleurs;
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Celles-ci pèseraient plus que le sable du rivage de la mer; mais, à ce qu'il me semble, mes paroles sont en efficacité.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 Car j'ai dans le corps les traits du Seigneur; leur courroux boit mon sang, et dès que je commence à discourir, ils me percent.
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Mais quoi! Est-ce sans motif que l'âne sauvage se met à braire, ou parce qu'il demande à manger? Et le bœuf mugit-il devant une crèche pleine de fourrage?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Mange-t-on le pain sans sel? Et trouve-t-on du goût aux paroles vaines?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 Pour moi, les aliments que l'on me sert, maintenant que je suis en proie à une colère qui ne me laisse point de repos, ont une odeur comme celle du lion.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Puisse ma prière être exaucée, puisse le Seigneur m'accorder ce que j'espère.
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 Le Seigneur a commencé, qu'il m'achève; qu'il mette fin à mes maux par une prompte mort.
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Puisse ma ville être un sépulcre dont je franchisse le mur d'un saut; je n'hésiterais pas; car je n'ai jamais éludé les saintes volontés de mon Dieu.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 Quelle est donc ma force pour subsister? Combien de temps encore ma vie me soutiendra-t-elle?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Ai-je la fermeté de la pierre? Mes chairs sont-elles d'airain?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Est-ce que je n'avais pas mis ma confiance en Dieu? Mais tout secours s'est éloigné de moi.
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 La miséricorde m'a méconnu; l'œil vigilant du Seigneur m'a méprisé.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 Mes proches ne m'ont point regardé; ils m'ont quitté rapides comme un torrent; ils ont passé près de moi comme un flot.
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Ceux qui me révéraient, je vois maintenant qu'ils s'étaient attachés à moi comme la neige ou la glace,
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 Qui fondent au retour de la chaleur, tellement que l'on ne peut retracer ce qu'elles étaient.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 C'est ainsi qu'ils m'ont tous abandonné; j'ai péri et je suis devenu un homme sans asile.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Regardez les chemins de Théman et les sentiers de Sadeba, vous qui voyez parfaitement.
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 Ils auront à rougir de honte, ceux qui se croient forts parce qu'ils possèdent des villes et des richesses.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Et vous, vous êtes venus à moi sans pitié; et quand vous avez vu ma plaie, vous avez eu peur.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Qu'y a-t-il? Vous ai-je demandés? Est-ce que j'attends de vous quelque force
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Pour me sauver de mes ennemis et me protéger contre les puissants?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Instruisez-moi et je garderai le silence; si j'ai erré en quoi que ce soit, ne tardez pas à me le dire.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Mais, à ce qu'il me semble, les discours d'un homme sincère sont sans efficacité, et je n'attends de vous aucune force.
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Vos réprimandes ne me rendront même pas le calme, et je suis importuné par le bruit de vos paroles.
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 En effet vous tombez sur un orphelin; vous vous jetez sur votre ami.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Puisque je vous ai vus en face, je ne dissimulerai rien.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Demeurez; entre nous point d'iniquité, remettez-vous d'accord avec un juste.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Car ma langue dit-elle rien qui ne soit équitable; et mon gosier donne-t- il passage à des paroles étudiées?
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?