< Job 38 >
1 Aussitôt qu'Elihou eut fini son discours, le Seigneur dit à Job à travers un nuage et un tourbillon:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Quel est celui qui me cache ses desseins? Il renferme des pensées en son cœur; croit-il qu'elles m'échapperont?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Ceins-toi les reins comme un homme; je vais te questionner: réponds-moi.
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Où étais-tu quand j'ai créé la terre? Déclare-le-moi si tu en as connaissance.
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Qui en a réglé les dimensions; le sais-tu? Qui a promené sur elle le cordeau pour en prendre la mesure?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Comment en a-t-on attaché les anneaux? Qui a posé sur elle la pierre angulaire?
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 Lorsque les astres ont paru, tous mes anges à haute voix m'ont applaudi.
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 J'ai renfermé la mer, j'ai placé des portes pour que, dans sa fureur, elle ne pût s'élancer hors des entrailles qui la contiennent.
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 Pour langes, je lui ai donné les brouillards, et pour vêtement les nuées.
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 J'ai fixé ses limites, je l'ai entourée de battants et de verrous.
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 Je lui ai dit: Tu iras jusque-là, tu n'iras pas plus loin; tes vagues se briseront sur toi-même.
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Est-ce de ton temps que j'ai disposé la lueur de l'aurore? et que l'étoile du matin a su qu'elle avait pour devoir
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 De secouer la terre, en la tenant par les deux ailes, et d'en faire tomber les impies?
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 Est-ce toi qui, ayant pris de l'argile, as formé un être vivant et l'as mis sur la terre, doué de parole?
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 As-tu ôté aux méchants la lumière, as-tu broyé les bras des orgueilleux?
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Es-tu descendu jusqu'au sources de la mer? As-tu marché dans les profondeurs de l'abîme?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Les portes de la mort s'ouvrent-elles sans t'effrayer? Peux-tu soutenir sans épouvante les regards des gardiens de l'enfer? ()
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 La vaste étendue que le ciel recouvre ne t'a-t-elle pas averti? Dis-le- moi, que penses-tu de sa grandeur?
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Quelle est la contrée où la lumière passe la nuit? Quel est le lieu où résident les ténèbres?
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 Pourrais-tu m'y conduire, en connais-tu le chemin?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Ne sais-je point que si dès lors tu étais né, tes jours ont été bien nombreux?
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 As-tu visité les trésors de la neige? As-tu vu les trésors de la grêle?
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 Les tiens-tu en réserve pour l'heure où se montreront tes ennemis, pour les jours de la guerre et des combats?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 D'où viennent les frimas ou le vent du midi qui souffle sous le ciel?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Quelle puissance a préparé la chute des pluies violente et la voie des cataclysmes
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 Qui fondent sur des contrées où il n'y a point d'hommes, sur des déserts où les mortels ne possèdent rien;
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 Qui fécondent des champs inhabités et leur font produire une herbe luxuriante?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Quel est le père de la pluie? Qui a produit les gouttes de la rosée?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 De quel sein est sortie la glace, d'où est né le givre du ciel
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 Qui descend comme l'eau coule? Quel est celui qui frappe de terreur les impies?
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Est-ce toi qui as enchaîné les pléiades et ouvert la clôture qui retenait Orion?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Feras-tu voir Mazuroth en son temps, et conduiras-tu sur sa chevelure l'étoile du soir elle-même?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Connais-tu les révolutions du ciel et ce qui arrive en même temps sur la terre?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Appelles-tu de la voix le nuage, t'obéit-il, en s'ébranlant verse-t-il des torrents d'eau?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Convoques-tu les éclairs? Viennent-ils en disant: Qu'y a-t-il?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Qui donc a enseigné aux femmes l'art de faire des tissus; qui les a douées de l'adresse d'y tracer des ornements divers?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Qui sait, en sa sagesse, dompter les nuages, et qui a courbé le ciel vers la terre?
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 Il a été malléable comme de la terre en poudre, et je l'ai consolidé comme un bloc de pierre.
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Chasseras-tu pour donner aux lions leur nourriture? Rempliras-tu l'âme des serpents?
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 Ils craignent dans leurs repaires, et ils se tiennent en embuscade au fond des forêts.
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Qui a préparé au corbeau sa pâture? car ses petits, en secouant leurs ailes, ont crié au Seigneur pour demander à manger.
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?