< Job 37 >
1 Ces réflexions ont troublé mon cœur, et il s'est écoulé hors de son enveloppe.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Ecoute les accents de la colère du Seigneur; songe à tout ce qui sortira de sa bouche.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Il règne sur tout ce que le ciel recouvre, et sa lumière s'étend sur les ailes de la terre.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Des voix s'élèveront derrière lui, elles se récrieront avec insolence; elles ne changeront pas ceux qui le servent, parce qu'ils l'auront compris.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Le Tout-Puissant fera retentir son tonnerre; il proclamera ses merveilles; car il a fait de grandes choses qui nous sont inconnues.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Il commande à la neige de tomber sur les champs; il règle l'hiver, la pluie, les tempêtes et les inondations qui signalent sa puissance.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Il appose son scel sur la main de l'homme, afin que chacun connaisse sa propre faiblesse.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Les bêtes fauves sont entrées en l'asile de l'homme; elles se sont reposées sur sa couche.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Les douleurs envahissent ses chambres les plus retirées; elles naissent au plus profond de son âme.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Le Tout-Puissant de son souffle répand la froidure; il dispose de l'eau comme il lui plaît.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 La nuée enveloppe aussi son élu, mais sa lumière la dissipe.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Et lui-même contourne selon sa volonté le cercle des travaux humains. Tout ce qu'il leur a prescrit,
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Tout ce qu'il a réglé sur la terre le manifestera, et les champs, et les plantes, et sa miséricorde.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Recueille tout ce que j'ai dit, Job; contiens-toi, et ne perds pas de vue la puissance du Seigneur.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Nous savons que Dieu, avant de créer les êtres, a séparé la lumière des ténèbres.
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Il prévoit la dispersion des nuages et la chute des méchants.
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Ta robe te tient chaud: c'est qu'il fait régner le calme sur la terre.
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 S'il te protège, tu consolideras ce qui tombe de vétusté; les choses les plus fortes, sans lui, sont comme la vision de l'onde qui s'écoule.
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 C'est pourquoi, apprends-le-moi, que lui dirons-nous? Cessons nos longs discours.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Est-ce qu'il n'y a pas le livre ou bien le scribe, afin qu'étant homme je sache garder le silence?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 La lumière n'est pas visible pour tous; la lèpre blanche s'attache aux vieux édifices, semblable à la faible lueur que Dieu répand sur les nuées.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 L'aquilon amène des nuages éclatants comme l'or; ils ont la splendeur et la gloire
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Du Tout-Puissant, et nous ne connaissons aucun vent qui lui soit semblable pour la force. Le souverain juge des choses justes croit-il devoir lui prêter la moindre attention?
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Aussi les hommes craindront Dieu; les sages en leur cœur auront crainte devant lui.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”