< Job 34 >

1 Et Elihou, continuant dit:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Ecoutez-moi, sages et savants; prêtez-moi une oreille attentive,
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Car l'oreille juge les paroles, comme le gosier goûte les aliments.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Servons-nous en pour décider; discernons entre elles ce qui est bon.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Job a dit: Je suis juste, le Seigneur m'a exclu du jugement;
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Il m'a rendu suspect par son arrêt; le trait a été violent, sans que j'eusse commis d'iniquité.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Quel est l'homme qu'autant que Job on ait abreuvé de railleries, comme on abreuve d'eau?
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 Et je n'ai point péché, je n'ai rien fait contre Dieu; je n'ai rien de commun avec les méchants; je n'ai point marché avec les impies.
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Ne tiens pas ce langage, car ce qui échappe à la surveillance de l'homme n'échappe pas à celle de Dieu;
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 C'est pourquoi, vous qui m'êtes unis par le cœur, soyez attentifs; puissé-je n'être point impie devant le Seigneur, et satisfaire à ce qui est juste devant le Tout-Puissant.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Qu'il rétribue chacun selon ses œuvres, et il saura bien trouver un homme sur sa voie.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Penses-tu Job, que le Seigneur fasse des choses vaines? Le Tout-Puissant fausse-t-il la justice, lui qui a créé la terre?
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Qui donc a fait l'étendue que le ciel recouvre et tout ce qui l'habite?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 S'il lui plaisait de s'abstenir, de retenir son souffle,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Toute chair au même instant périrait; tout homme retournerait à la terre dont il a été formé.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 S'il ne t'a pas averti, écoute ce que je vais te dire, que tes oreilles le recueillent.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Considère toi-même celui qui hait les pervers, celui qui extermine les méchants, celui qui est éternellement juste.
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Celui qui ne craint pas d'appeler un roi impie; ni de dire aux grands: vous êtes corrompus, vous vivez dans le péché.
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Celui qui n'a aucun égard pour le rang; qui ne sait point honorer la force ni lui rendre des respects.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 A prier un homme qui pratique l'iniquité, qui méconnaît les pauvres, on n'obtiendra que des choses vaines.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Mais Dieu voit les œuvres des mortels; rien de ce qu'ils font ne lui est caché.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Il n'est point de lieu où les pervers puissent se soustraire à ses regards.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Il ne s'y prend pas à deux fois pour juger un homme.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Le Seigneur surveille tout; il est l'auteur d'une multitude de merveilles incompréhensibles et glorieuses.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Il connaît les travaux des humains, sur eux il ramènera la nuit et ils seront humiliés.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Il a éteint les impies; il ne lui est point échappé
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Qu'ils s'étaient écartés de la loi de Dieu, et qu'ils avaient méconnu ses préceptes.
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 Ils avaient contraint les pauvres de l'invoquer, et il exaucera toujours les indigents.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Seul il donne la paix, et qui donc fera condamner celui à qui il l'accorde? S'il cache son front, qui le verra? Il juge les nations comme les individus.
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Il place sur le trône un roi hypocrite, à cause des caprices du peuple.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Il en est qui disent au Tout-Puissant: Si j'ai pris, je ne retiendrai rien en gage.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Je ne puis voir par moi-même; faites-moi connaître si j'ai commis quelque iniquité, et je ne recommencerai pas.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Est-il juste que vous m'en punissiez; ne deviez-vous pas la prévenir; n'est-ce pas vous qui choisissez et non moi? Ce que vous savez, déclarez-le.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 S'il est vrai que des cœurs intelligents peuvent parler en ces termes, d'autre part c'est à un homme sage que je parle, et il m'écoute.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job n'a point raisonné en homme habile, ses discours ne montrent pas de savoir.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 O Job, réfléchis donc; ne réponds pas derechef à la manière des insensés.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 De peur que nous n'ajoutions pas à nos fautes; car il nous sera imputé à péché de nous étendre en longs discours devant le Seigneur.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >