< Job 19 >
2 Jusqu'à quand fatiguerez-vous mon âme et me tuerez-vous de vos discours?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Sachez seulement que le Seigneur m'a traité de la sorte. Persuadez-moi, et ne vous attachez pas tant à me faire honte.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 En vérité, j'ai sans doute failli; l'erreur réside avec moi. Dis-moi donc quelque chose que j'ignore, sans quoi je m'égarerai en mes réponses, et elles manqueront d'à propos.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 Cessez, car vous vous grandissez pour m'assaillir, et vous m'accablez d'outrages.
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Mais ne perdez donc pas de vue que c'est le Seigneur qui m'a troublé, et qu'il a élevé contre moi ses murailles.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 De vos injures je ne ferais que rire, et je ne dirais mot; quand je crierais, je n'obtiendrais pas de jugement.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Mais des remparts m'étreignent et je ne puis les traverser, et l'obscurité règne devant moi.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Le Seigneur m'a ravi toute gloire, il a ôté la couronne que je portais sur la tête.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 Il m'a tiraillé dans tous les sens et j'ai succombé; il a abattu comme un arbre toute mon espérance.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 Il a déployé contre moi une colère terrible; il m'a regardé comme un ennemi.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 Ses épreuves me sont venues toutes ensemble; ses embuscades étaient placées sur toutes mes voies.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 Mes frères se sont éloignés; ils m'ont préféré des inconnus; mes amis n'ont eu aucune compassion.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 Mes plus proches m'ont laissé sans soins; et ceux qui savaient mon nom l'ont oublié.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 Mes voisins, les servantes de ma maison; je suis un étranger pour eux.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 J'ai appelé mon serviteur, il n'est point venu; ma bouche est devenue suppliante.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 J'ai imploré ma femme, j'ai demandé les fils de mes concubines en les flattant,
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Ils m'ont répudié pour toujours; si je me relève, ils se récrient contre moi.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 J'ai été pour eux un objet d'horreur pour ceux qui m'ont vu; j'ai pour ennemis ceux que j'avais aimés.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Mes chairs sous ma peau pourrissent, mes os sont entre les dents qui les rongent.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Ayez pitié de moi, ayez pitié de moi, ô mes amis, car c'est la main du Seigneur qui m'a touché.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Pourquoi me poursuivez-vous comme me poursuit le Seigneur? Voulez-vous vous repaître de ma chair?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Qui donc écrira mes plaintes pour les déposer en un livre impérissable?
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 Qui les gravera au burin sur la pierre ou le plomb?
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 Car je sais que de toute éternité existe celui qui doit me délivrer, et sur la terre
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 Faire revivre ma peau pour que je jouisse de ces choses...car c'est le Seigneur qui a fait ces choses
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Qu'en moi-même je sais; que mon œil a vues, et non l'œil d'autrui; et qui déjà sont accomplies en mon sein.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Et si vous dites: Quel langage tiendrons-nous devant lui? quel sujet de discours trouverons-nous en sa personne?
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Prenez garde aux choses cachées; songez que la colère tombera aussi sur les méchants; et alors ils sentiront où est la matière dont ils sont formés.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”