< Job 11 >

1 Or Sophar le Minéen, prenant la parole, dit:
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Celui qui parle tant, à son tour écoutera: l'homme verbeux semble-t-il juste? Le fils de la femme qui vit peu est béni.
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Ne te répands pas en longs discours, puisque nul ne plaide contre toi.
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 Surtout, garde-toi de dire: Je suis pur dans mes œuvres; je suis irréprochable devant Dieu.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 Car par quel moyen le Seigneur pourrait-il te répondre et ouvrir les lèvres en même temps que toi?
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 Ensuite il te donnera la force du sage deux fois plus que ne l'ont ceux qui te ressemblent; tu reconnaîtras alors que le Seigneur t'a rétribué justement, selon tes péchés.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Découvriras-tu les traces du Seigneur? Es-tu parvenu jusqu'aux dernières limites de ce que le Tout-Puissant a créé?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 Le ciel est haut, que feras-tu? L'abîme est profond, que feras-tu? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 Les dimensions de la terre, l'étendue des mers ne te sont-elles pas inconnues?
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 S'il plaît au Seigneur de bouleverser toutes ces choses, qui lui dira: Qu'avez-vous fait?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 Seul il connaît les œuvres des déréglés; s'il voit des choses vaines, il ne tiendra point de n'en rien savoir.
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 L'homme nage au hasard s'il n'a d'autres guides que des raisonnements; le mortel né de la femme est isolé comme l'âne sauvage.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 Si tu as purifié ton cœur, élève tes mains vers Dieu.
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 Si tes mains sont chargées de quelque iniquité, hâte-toi de la rejeter au loin; elle ne doit point passer la nuit dans ta demeure.
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 Alors ton visage brillera comme une onde pure; tu ôteras tes vêtements sordides, et tu n'éprouveras plus de crainte.
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Tu oublieras tes souffrances; elles auront passé comme une vapeur, et ta raison sera raffermie.
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 Ta prière ressemblera à l'étoile qui annonce l'aurore; ta vie se lèvera au Midi.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 Tu seras plein de confiance, parce que l'espérance ne t'aura pas abandonné; de tes soucis, de tes peines naîtra la paix.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Tu jouiras du repos et n'auras plus d'ennemis; la foule inconstante des hommes te reviendra.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 Cependant le salut délaissera les impies; leur espoir sera leur perte, et leurs yeux fondront en larmes.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< Job 11 >