< Jérémie 4 >
1 Si Israël revient à moi, dit le Seigneur, s'il se convertit, s'il retire de sa bouche ses abominations et s'il craint devant ma face,
“In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
2 Et s'il jure, Vive le Seigneur avec sincérité, équité et justice, les nations seront bénies en lui, et loueront Dieu dans Jérusalem.
kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
3 Car ainsi dit le Seigneur aux hommes de Juda et aux habitants de Jérusalem: Labourez une terre neuve, et ne semez point parmi les chardons.
Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
4 Circoncisez-vous pour votre Dieu, circoncisez la dureté de vos cœurs, hommes de Juda, et vous, habitants de Jérusalem, de peur que ma colère ne jaillisse comme une flamme et ne vous brûle, et que nul ne soit là pour l'éteindre à la vue de la malice de vos péchés.
Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
5 Annoncez à Juda, et qu'on vous entende en Jérusalem; dites: Donnez le signal de la trompette sur la terre; criez fort et dites: Rassemblez-vous tous, et entrez dans les villes fortifiées.
“Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
6 Emportez tout ce que vous pourrez; réfugiez-vous dans Sion; hâtez-vous, ne faites point de halte; car moi, je vais vous amener de l'aquilon des maux et de grands brisements de cœur.
Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
7 Le lion est sorti de son antre; il s'est élancé exterminant les nations, et il est parti de sa contrée pour faire de la terre une solitude; et les cités seront abattues, parce qu'il n'y aura plus d'habitants.
Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
8 C'est pourquoi ceignez-vous de cilices, frappez-vous la poitrine, jetez de grands cris; car la colère du Seigneur ne s'est point détournée de vous,
Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
9 Et en ce jour, dit le Seigneur, périra le cœur du roi et le cœur des princes; les prêtres seront saisis de stupeur, et les prophètes seront confondus.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
10 Et je dis: O Seigneur, maître, est-ce donc que vous avez trompé ce peuple et Jérusalem, disant: La paix règnera, et voilà que le glaive a pénétré jusqu'à leur âme!
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
11 En ce temps-là, on viendra dire à ce peuple et à Jérusalem: Un esprit d'erreur souffle au désert; la voie de la fille de mon peuple ne conduit ni à la pureté ni à la sainteté.
A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
12 Mais un souffle de plénitude me viendra; et alors moi je dirai mes jugements contre eux.
iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
13 Voilà qu'il va venir comme une nuée, et son char sera comme un vent impétueux, ses chevaux plus rapides que l'aigle: Malheur à nous! car nous serons accablés de souffrances.
Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
14 Jérusalem, lave ton cœur de tes méchancetés, afin que tu sois sauvée. Jusques à quand resteront-elles en ton cœur, les pensées qui causent tes maux.
Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
15 Car la voix du messager de malheur viendra de Dan, et on entendra des cris de douleur des montagnes d'Éphraïm.
Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
16 Vous étés averties, nations; voilà qu'ils sont arrivés, proclamez-le dans Jérusalem; leurs bandes viennent d'une terre lointaine, et elles ont poussé des cris contre la ville de Juda.
“A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
17 Comme les gardiens d'un champ, ils font une enceinte autour d'elle; parce que tu m'as négligé, dit le Seigneur.
Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
18 Tes voies et tes pensées ont attiré sur toi de tels maux, parce que ta méchanceté a été pleine d'amertume, et a pénétré jusqu'au fond de ton cœur.
“Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
19 Mes entrailles, je souffre en mes entrailles et dans les sensations de mon cœur; mon âme est agitée de transports; mon cœur est déchiré. Je ne garderai point le silence; car mon âme a entendu le son de la trompette et les cris de la guerre.
Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
20 Et de sa profonde misère elle appelle le secours de la contrition; car toute la terre a été dans la désolation, le tabernacle a été soudain désolé, et les tentures en ont été dispersées.
Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
21 Jusques à quand verrai-je mes guerriers en fuite, et entendrai-je le son de la trompette?
Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
22 Les princes de mon peuple ne m'ont point reconnu; ce sont des fils insensés et privés d'intelligence; ils sont habiles pour mal faire, et ne savent pas faire le bien.
“Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
23 J'ai regardé la terre, et voilà qu'il n'y avait plus rien; j'ai regardé le ciel, et ses astres n'étaient plus.
Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
24 J'ai vu les montagnes, et elles étaient tremblantes, toutes les collines pleines de troubles.
Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
25 J'ai regardé, et voilà qu'il n'y avait pas un homme, et tous les oiseaux du ciel étaient effarouchés.
Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
26 J'ai vu, et voilà que le Carmel était désert, et toutes les villes brûlées par le feu, devant la face du Seigneur; elles avaient toutes été effacées devant la face de sa colère.
Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
27 Or voici ce que dit le Seigneur: Toute la terre sera déserte; mais je ne la ferai point périr tout entière.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
28 Que la terre pleure sur ces maux; que le ciel s'obscurcisse en ses hauteurs; j'ai parlé et je ne me repentirai pas; je me suis élancé en avant, et je ne me détournerai pas du but.
Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
29 Aux cris du cavalier, à l'aspect de l'arc tendu, toute la terre s'est enfuie; ils sont entrés dans les cavernes, ils se sont cachés dans les bois, ils sont montés sur les rochers, Toute ville a été abandonnée; il n'y reste pas un homme.
Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
30 Et toi, que feras-tu? Tu auras beau te revêtir d'écarlate, mettre tes joyaux d'or, teindre en noir tes sourcils; tu te seras parée en vain. Tes amants t'ont repoussée, c'est ta vie qu'ils demandent.
Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
31 J'ai entendu tes cris comme ceux d'une femme en mal d'enfant, tes gémissements comme ceux d'une mère qui enfante pour la première fois; la voix de la fille de Sion sera brisée, et elle laissera tomber ses mains. Malheur à moi! dira-t-elle, mon âme est défaillante au milieu des morts.
Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”