< Jérémie 16 >
1 Et tu ne prendras point femme, dit le Seigneur Dieu d'Israël,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Et il ne te naîtra ni fils ni fille en ce lieu.
“Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
3 Car voici ce que dit le Seigneur sur les fils et les filles nés en ce lieu, et sur leurs mères qui les auront mis au monde, et sur leurs pères qui les auront engendrés en cette terre:
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
4 Ils mourront d'une mort cruelle; on ne pleurera pas sur eux; ils ne seront pas ensevelis; ils resteront en exemple sur la face de la terre; ils seront pour les bêtes de la terre et les oiseaux du ciel; ils périront par le glaive ou seront consumés par la faim.
“Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
5 Voici ce que dit le Seigneur: N'entre pas dans leurs festins funèbres; ne va pas te frapper la poitrine et ne pleure pas sur eux; car j'ai retiré ma paix de ce peuple.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
6 On ne pleurera point sur eux; on ne se fera pas d'incisions; on ne se rasera pas la tête;
“Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
7 On ne rompra point dans leur deuil les pains de la consolation sur un mort; on ne fera pas boire le fils dans le calice de consolation, sur son père ou sa mère.
Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
8 Et toi, tu n'entreras pas dans la maison du banquet pour t'y asseoir, et manger et boire avec eux.
“Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
9 Car ainsi parle le Seigneur Dieu d'Israël: Voilà qu'en ce lieu, devant vous et de vos jours, je ferai taire la voix des réjouissances et la voix des fêtes, la voix du jeune époux et la voix de l'épousée.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
10 Et ceci arrivera lorsque tu feras connaître à ce peuple toutes ces paroles, et qu'il te dira: Pourquoi le Seigneur a-t-il dit tant de mal sur nous? Quelle est notre iniquité? quel péché avons-nous commis devant le Seigneur notre Dieu?
“Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
11 Tu leur diras: C'est en punition de ce que vos pères m'ont abandonné, dit le Seigneur, et ils ont marché à la suite des dieux étrangers; ils les ont servis, et les ont adorés; ils m'ont abandonné, et n'ont point gardé ma loi.
Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
12 Et vous-mêmes vous avez fait le mal plus que vos pères; et voilà que chacun de vous court après ce qui plaît à son cœur perverti, si bien qu'on ne m'obéit plus.
Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
13 Et je vous rejetterai de cette terre, et je vous enverrai en une terre que vous n'avez connue ni vous ni vos pères, où vous servirez d'autres dieux, et de ceux-là n'attendez aucune miséricorde.
Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
14 A cause de cela, voilà que viennent les jours, dit le Seigneur, où ils ne diront plus: Vive le Seigneur, qui a ramené de la terre d'Égypte les fils d'Israël!
“Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
15 Mais, vive le Seigneur, qui a ramené la maison d'Israël de la terre du nord et de toutes les contrées où ils avaient été transportés! et je les rétablirai dans l'héritage que j'ai donné à leurs pères.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
16 Voilà que je vais envoyer maints pêcheurs, dit le Seigneur Dieu, et ils les pêcheront, et après cela j'enverrai maints chasseurs, et ils leur feront la chasse sur toutes les montagnes, sur toutes les collines, dans toutes les crevasses des rochers.
“Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
17 Car j'ai les yeux sur toutes leurs voies; et leurs iniquités n'ont point été cachées à mes yeux.
Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
18 Et je donnerai une double rétribution à leurs méchancetés et aux péchés dont ils ont souillé celte terre, avec les cadavres mêmes de leurs abominations et avec les iniquités qu'ils ont faites en mon héritage.
Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
19 Seigneur, dans les jours de calamités, vous êtes ma force, mon appui, mon refuge. Les gentils viendront à vous des extrémités de la terre, et ils diront: Quelles idoles trompeuses ont possédées nos pères! Il n'y avait en elles aucun secours.
Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
20 Est-ce que des dieux peuvent être faits par l'homme? et encore ce ne sont pas des dieux.
Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
21 A cause de cela, en ce temps-là, je leur montrerai ma main, et je leur ferai connaître ma puissance, et ils sauront que mon nom est le Seigneur.
“Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.