< Jérémie 14 >
1 Et la parole du Seigneur vint à Jérémie au sujet de la sécheresse.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
2 La Judée a pleuré, et ses portes sont solitaires, et la terre est pleine de ténèbres, et un cri s'est élevé en Jérusalem.
“Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
3 Et les plus grands ont envoyé les plus petits puiser de l'eau. Ceux-ci sont allés aux puits; mais ils n'ont point trouvé d'eau, et ils sont revenus les cruches vides.
Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
4 Et les travaux de la terre ont péri, parce qu'il ne pleuvait pas; les laboureurs ont été confondus, et ils se sont voilé la tête;
Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
5 Et les biches ont mis bas dans la plaine, et elles ont abandonné leurs faons, parce qu'il n'y avait point d'herbe.
Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
6 Les ânes sauvages se sont arrêtés dans les vallons ombragés, et ils ont aspiré l'air; leurs yeux ont défailli, parce qu'il n'y avait point de fourrage.
Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
7 Nos péchés se sont élevés contre nous, Seigneur; prenez soin de nous à cause de vous-même; car nos péchés contre vous sont nombreux, c'est contre vous que nous avons péché.
Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
8 Seigneur, vous êtes l'espérance d'Israël; c'est vous qui sauvez au temps de l'affliction. Pourquoi êtes-vous devenu à notre égard comme un passager sur la terre, ou comme un indigène allant dans une hôtellerie.
Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
9 Serez-vous comme un homme endormi ou comme un homme impuissant à sauver? Vous êtes avec nous, Seigneur, et votre nom est le nom qui nous est donné; ne nous oubliez plus.
Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
10 Ainsi dit le Seigneur à ce peuple: Ils ont aimé à remuer leurs pieds, et ils n'y ont pas mis de mesure, et Dieu ne les a pas fait prospérer; maintenant il va se souvenir de leurs iniquités.
Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
11 Et le Seigneur me dit: Ne me prie pas en faveur de ce peuple pour le bénir.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
12 Car lors même qu'ils jeûneraient, je n'exaucerai point leur prière; et s'ils m'offrent des holocaustes et des victimes, je ne les agréerai point. Car moi, je les exterminerai par le glaive, la famine et la mort.
Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
13 Et je répondis: O vous, Seigneur vivant, voilà que leurs prophètes prophétisent, et disent: Vous ne verrez pas de glaive; il n'y aura pas de famine parmi vous; car je donnerai à cette terre et à ce lieu la vérité et la paix.
Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
14 Et le Seigneur me dit: Leurs prophètes prophétisent faussement en mon nom; je ne les ai point envoyés; je ne leur ai rien commandé; je ne leur ai rien dit. Ils vous prophétisent d'après des visions mensongères, des augures, des présages, des caprices de leur cœur.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
15 À cause de cela, dit le Seigneur, et pour ce qui regarde les prophètes qui prophétisent faussement en mon nom, et que je n'ai point envoyés, et qui disent: Il n'y aura en cette terre ni glaive ni famine, ces prophètes mourront d'une maladie cruelle, et ils seront consumés par la faim,
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
16 Et le peuple pour qui ils prophétisent, gisant dans les rues de Jérusalem, périra par le glaive ou la famine; et nul n'ensevelira les morts, ni leurs femmes, ni leurs fils, ni leurs filles, et je ferai refluer sur eux leur propre méchanceté.
Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
17 Et tu leur diras cette parole: Que vos yeux versent des larmes nuit et jour, et que vos pleurs ne s'arrêtent pas; car la fille de mon peuple a été écrasée et broyée, et sa blessure est pleine de douleurs.
“Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
18 Si je sors dans la plaine, voilà des cadavres frappés par le glaive; si je rentre dans la ville, voilà les horreurs de la famine, et le prêtre et le prophète sont allés en une terre qu'ils ne connaissaient pas.
In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
19 Est-ce que vous avez répudié Juda; et votre âme s'est-elle éloignée de Sion? Pourquoi nous avez-vous frappés, et n'y a-t-il pas pour nous de remède? Nous attendions la paix, et il n'est rien venu d'heureux; la guérison, et voilà le trouble.
Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
20 Nous reconnaissons nos péchés et les iniquités de nos pères; car c'est contre vous que nous avons péché.
Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
21 Cessez, en faveur de votre nom, de détruire le trône de votre gloire; souvenez-vous et ne rompez point votre alliance avec nous.
Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
22 Y a-t-il une seule idole des nations qui fasse tomber la pluie? Et si le ciel nous accorde ses largesses, n'est-ce point par vous? Aussi nous espérons en vous, Seigneur; car c'est vous qui avez fait toutes ces choses.
Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.