< Isaïe 8 >
1 Et le Seigneur me dit: Prends avec toi un grand livre tout neuf, et avec le stylet d'un écrivain écris sur ce livre que l'on ait à recueillir promptement du butin; car voici l'heure.
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 Et assure-toi pour moi de deux témoins fidèles, Urie, et Zacharie, fils de Barachie.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 Et je m'approchai de la prophétesse, et elle conçut, et elle enfanta un fils, et le Seigneur me dit: Appelle-le de ce nom: Dépouille vite, pille promptement.
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 Car, avant que l'enfant sache dire le nom de son père et de sa mère, il s'emparera des richesses de Damas et des dépouilles de Samarie devant le roi des Assyriens.
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 Et le Seigneur continua de me parler:
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 Puisque ce peuple ne veut point de l'eau de Siloé, qui coule si paisible, mais qu'il veut avoir pour roi Basin et le fils de Romélie;
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 Voilà que le Seigneur amène sur vous l'eau d'un fleuve profond et impétueux, le roi des Assyriens et sa gloire; et il s'élèvera sur toutes vos vallées, et il foulera aux pieds tous vos remparts.
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 Et il enlèvera de la Judée tout homme capable de lever la tète, tout guerrier capable de faire un exploit. Et son camp sera assez vaste pour couvrir toute l'étendue de ton pays; mais Dieu est avec nous!
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Apprenez ceci, ô nations, vous êtes vaincues; prêtez-moi l'oreille jusqu'aux extrémités de la terre; vous êtes fières de vos forces, et vous êtes vaincues; et si vous réunissez de nouvelles forces vous serez de nouveau vaincues.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 Et quels que soient vos conseils, le Seigneur les dissipera; et quelles que soient vos paroles, elles ne s'accompliront point; car le Seigneur est avec nous.
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 Voici ce que dit le Seigneur: Que d'une main ferme on s'éloigne de la voie de ce peuple;
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 Que l'on ne dise pas: Cela est dur. Toute parole que dit ce peuple est toujours dure. N'aie cependant aucune crainte, et ne sois point dans le trouble.
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 Ne sanctifie que le Seigneur, et que seul il soit l'objet de ta crainte.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 Et si tu mets en lui ta confiance, il sera ta sanctification; et tu ne te heurteras pas à lui comme à une pierre d'achoppement, comme à une roche qui croule. Mais les maisons de Jacob sont dans un piège, et les habitants de Jérusalem sont dans une fosse.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 C'est pourquoi beaucoup d'entre eux seront sans force, et ils tomberont, et ils seront brisés; ils approcheront du filet, et ils y seront pris.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Alors apparaîtront manifestement ceux qui ont été marqués d'un sceau pour n'avoir pas appris la loi.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 Et je dirai: J'attendrai Dieu, qui a détourné sa face de la maison de Jacob, et je mettrai en lui ma confiance.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Et moi, me voici avec les fils que Dieu m'a donnés. Et il y aura des signes et des prodiges dans la maison d'Israël, envoyés par le Seigneur Dieu des armées, qui habite sur la montagne de Sion.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 Et si l'on vous dit: Consultez les magiciens et ceux qui font sortir leur voix de la terre, et les diseurs d'imposture qui parlent du ventre, répondez: Est-ce que chaque nation ne consulte pas son Dieu? Pourquoi consulter les morts au sujet des vivants?
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 Car Dieu a donné une loi pour qu'on y ait recours, et qu'on dise: Ce n'est pas selon ce précepte, qui interdit de donner pour cela des présents.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 Et il viendra sur vous une cruelle famille, et, quand vous aurez faim, il arrivera que vous serez dans l'affliction, et vous maudirez le prince et les coutumes de vos ancêtres; et le peuple lèvera les yeux au ciel,
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 Puis il les abaissera vers la terre; et voilà qu'il y aura détresse et ténèbres, tribulation et angoisses; et les ténèbres seront telles qu'on ne verra plus;
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.