< Isaïe 44 >

1 Maintenant écoute, Jacob mon serviteur, Israël mon élu.
“Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
2 Voici ce que dit le Seigneur Dieu qui t'a créé, qui t'a formé dès les entrailles de ta mère: Tu seras encore secouru; ne crains pas, mon serviteur Jacob, mon bien-aimé, Israël mon élu.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
3 Je donnerai de l'eau dans leur soif à ceux qui traversent la terre aride; je ferai descendre mon esprit sur ta semence, et mes bénédictions sur tes enfants.
Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
4 Et ils croîtront comme l'herbe entre les ruisseaux, comme le saule sur le bord d'une eau courante.
Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
5 Celui-ci dira: Je suis de Dieu. Celui-là se glorifiera du nom de Jacob; cet autre écrira de sa main: Je suis de Dieu, et se glorifiera du nom d'Israël.
Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
6 Voici ce que dit le Dieu, roi d'Israël, le Dieu des armées, rédempteur de Jacob: Je suis le premier, et je suis le dernier; hormis moi, il n'est point de Dieu.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
7 Qui est semblable à moi? Que celui-là se présente; qu'il rappelle, proclame et m'explique ce que j'ai fait pour l'homme depuis le commencement des siècles; qu'ils vous fassent connaître d'avance les choses de l'avenir.
Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
8 Ne dissimulez pas, ne divaguez point, dès le commencement n'avez-vous pas ouï cela de vos oreilles? Ne vous l'ai-je pas déclaré? Vous êtes mes témoins; hormis moi, il n'est point de Dieu. Et ils n'existaient pas ainsi,
Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
9 Les artisans, les sculpteurs d'idoles, tous insensés, faisant à leur fantaisie des choses qui ne leur serviront de rien. Mais ils seront confondus.
Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
10 Tous ceux qui façonnent un dieu, et qui sculptent des choses inutiles,
Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
11 Tous les auteurs de ces vanités ont tous disparu; rassemblez ces hommes sourds, tenez-les réunis; que tous ensemble ils soient humiliés, qu'ils soient tous confondus.
Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
12 L'artisan a aiguisé le fer; il a pris la hache, il a employé la tarière; il a fait son œuvre par l'effort de ses bras; et il aura faim, et il sera sans force, et il n'aura pas d'eau à boire. Ayant choisi
Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
13 L'arbre, l'artisan l'a dressé avec la mesure, l'a collé et ajusté; puis il lui a donné la forme d'un mortel et la beauté d'un homme pour le placer dans un temple.
Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
14 Il a abattu un arbre de la forêt, un arbre qu'avait planté le Seigneur, un pin que la pluie avait fait croître
Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
15 Pour qu'il fût brûlé par les hommes; il en a pris une part et s'en est chauffé; sur la braise ils ont cuit des pains; et avec le reste ils ont façonné des dieux, et ils les adorent.
Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
16 Il n'en a pas brûlé la moitié; et sur cette moitié il s'est servi des braises pour faire cuire des pains et rôtir des chairs qu'il a mangées; il s'est rassasié, et après s'être chauffé il a dit: il m'est doux de me chauffer et de voir la flamme.
Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
17 Et avec le reste il a sculpté un dieu; et il l'adorera et le priera, disant: protège-moi, car tu es mon Dieu.
Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
18 Ils n'ont rien su comprendre; leurs yeux obscurcis ne voient plus; leurs cœurs ne sentent rien.
Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
19 Et cet homme n'a point raisonné en son âme; il n'a pas su comprendre qu'il a brûlé la moitié de l'arbre, et que sur ses braises il a cuit du pain, il a rôti des chairs dont il s'est nourri, et qu'avec le reste il a fabriqué une abomination qu'on adore.
Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
20 Sache que le cœur de ces dieux n'est que cendre; mais ils sont égarés, et nul d'eux ne peut sauver son âme. Voyez, et ne direz-vous pas: Cette œuvre de ma main n'est qu'un mensonge?
Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
21 Souviens-toi de ces choses, ô Jacob, ô Israël, car tu es mon serviteur; je t'ai créé pour me servir; ô Israël, ne m'oublie pas.
“Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
22 Car voilà que j'ai effacé tes péchés comme un nuage; et ton iniquité, comme une vapeur. Reviens à moi, et je te rachèterai.
Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
23 Cieux, réjouissez-vous. Dieu a eu pitié d'Israël; sonnez de la trompette, fondements de la terre; montagnes, poussez des cris d'allégresse; et vous, collines, et vous, arbres qui les couvrez, le Seigneur a racheté Jacob, et Israël sera glorifié.
Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
24 Voici ce que dit le Seigneur, qui t'a racheté et qui t'a formé dès les entrailles de ta mère: Je suis le Seigneur qui accomplit toutes choses; seul j'ai tendu les cieux et j'ai affermi la terre.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
25 Quel autre que moi dissipera les signes des magiciens et détournera des cœurs les prédictions des devins? Je suis le Seigneur; c'est moi qui renverse la sagesse des sages, et qui rends vains leurs conseils.
wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
26 C'est moi qui affermis la parole de mon serviteur, qui confirme les conseils de mes messagers, et qui dis à Jérusalem: Tu seras repeuplée; et aux villes de l'Idumée: Vous serez rebâties, et vos champs dévastés refleuriront.
wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
27 C'est moi qui dis à l'abîme: Tu seras épuisé, et je dessècherai tes fleuves.
wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
28 C'est moi qui dis à Cyrus: Sois prudent, et tu accompliras toutes mes volontés; et qui dis à Jérusalem: Tu seras rebâtie, et je jetterai les fondations de mon saint temple.
wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’

< Isaïe 44 >