< Isaïe 28 >
1 Malheur à la couronne d'orgueil, ô mercenaires d'Éphraïm; fleur qui tombe de sa gloire sur la cime de la montagne fertile; hommes ivres sans vin.
Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
2 Voilà que la colère du Seigneur est violente et terrible, comme la grêle tombant où il n'y a point d'abri, tombant avec force comme une inondation qui ravage une campagne; il donnera le repos à la terre. Sous les mains
Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
3 Et les pieds sera foulée votre couronne d'orgueil, ô mercenaires d'Éphraïm!
Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
4 Et la fleur détachée de l'espérance de votre gloire, sur la cime de la haute montagne, sera comme le premier fruit mûr du figuier; celui qui l'aura vu, avant que sa main l'ait saisi, désirera le dévorer.
Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
5 Ce jour-là, le Seigneur Dieu des armées sera une couronne d'espérance, et comme une guirlande de gloire, pour le reste de son peuple.
A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
6 Ils seront restés en esprit de justice pour rendre la justice, et détruire les forces de ceux qui les entravent.
Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
7 Car ils ont été entraînés au péché par le vin; ils ont été égarés par les boissons fermentées; prêtres et prophètes ont perdu le sens, à cause des boissons fermentées; ils ont été absorbés par le vin; ils ont chancelé dans l'ivresse, ils ont erré: telle est ma vision.
Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
8 La malédiction consumera leurs conseils; car leurs conseils sont nés de la cupidité.
Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
9 A qui avons-nous prédit ces maux? à qui avons-nous porté ce message? A vous qui venez d'être sevrés, vous qu'on vient de retirer de la mamelle.
“Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
10 Attendez affliction sur affliction, espérance sur espérance; encore un peu de temps, encore un peu de temps.
Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
11 Avec des lèvres dédaigneuses, en une langue étrangère, Dieu parlera à ce peuple.
To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
12 Il lui dira: Voici le repos de celui qui a faim, et voilà son affliction; et ils n'ont pas voulu écouter.
waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
13 Et la prédiction du Seigneur sera pour eux: affliction sur affliction, espérance sur espérance; encore un peu de temps, encore un peu de temps; afin qu'ils partent, et qu'ils tombent à la renverse; et ils seront broyés, et ils seront pris au piège, et ils périront.
Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
14 A cause de cela, écoutez la parole du Seigneur, hommes opprimés, et vous, princes de ce peuple qui est en Jérusalem.
Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
15 Vous disiez: Nous avons fait un pacte avec l'enfer, et des conventions avec la mort; s'il passe un tourbillon impétueux, il ne viendra pas sur nous; nous avons fait du mensonge notre espérance, nous serons abrités par le mensonge. (Sheol )
Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol )
16 A cause de cela, ainsi dit le Seigneur, voilà que je mets dans les fondations de Sion une pierre de grand prix, une pierre choisie et précieuse; c'est la pierre angulaire et honorable des fondations; et celui qui croira en elle ne sera point confondu.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
17 Et je rendrai un jugement, pour qu'il soit une espérance; et ma miséricorde sera pesée avec mesure; et vainement ils seront appuyés sur le mensonge; si le tourbillon a passé près de vous,
Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
18 Est-ce parce que Dieu n'a pu rompre votre alliance avec la mort, ni l'espérance que vous placiez sur l'enfer? Si le tourbillon impétueux passe, il vous foulera aux pieds; (Sheol )
Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol )
19 S'il passe, il vous prendra dès l'aurore; dès l'aurore il passera, et il durera tout le jour, et la nuit votre attente sera pire encore. Instruisez-vous à comprendre,
A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
20 O vous qui êtes tourmentés, vous dites: Nous ne pouvons combattre, nous sommes trop faibles pour nous rassembler.
wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
21 Le Seigneur s'élèvera contre vous, comme contre la montagne des impies, et il se tiendra dans la vallée de Gabaon; et il fera ses œuvres avec colère, œuvres d'amertume; et il agira avec un courroux qui lui est étranger, et il vous frappera d'une plaie qui lui est étrangère
Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
22 Gardez-vous de vous réjouir et de rendre plus forts vos liens; car j'ai appris du Seigneur Dieu des armées les œuvres accomplies et prochaines qu'il fera par toute la terre.
Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
23 Prêtez l'oreille, écoutez ma voix, soyez attentifs et recueillez mes paroles.
Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
24 Est-ce que le laboureur laboure toute la journée? Ne prépare-t-il pas la semence avant de travailler à la terre?
Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
25 Après en avoir aplani la surface, ne sème-t-il pas de la poivrette et du cumin? Ne sème-t-il pas ensuite du froment, de l'orge, du millet, de l'épeautre, selon ses desseins?
Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
26 Or tu seras instruit par le jugement de ton Dieu, et tu te réjouiras.
Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
27 Car la poivrette n'est point nettoyée durement; on ne fait point passer les roues d'un char sur le cumin, mais on bat la poivrette avec une verge;
Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
28 Et on mange le cumin avec du pain. Ainsi moi, je ne serai pas éternellement irrité contre vous, et la voix de mon amertume ne vous écrasera point toujours.
Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
29 Tous ces signes viennent du Seigneur des armées; méditez-les, et rejetez toute vaine consolation.
Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.