< Isaïe 23 >

1 Vision sur Tyr. Poussez des cris de douleur, vaisseaux de Carthage; car elle a péri, et ses matelots ne reviendront plus de la terre des Citiens; elle a été emmenée captive.
Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
2 A qui sont-ils devenus semblables ces habitants de l'île, ces trafiquants de Phénicie, qui traversaient la mer
Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
3 Sur les grandes eaux, cette race de marchands? Comme une moisson qu'on emporte, ainsi ils trafiquaient des nations.
A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
4 Rougis, Sidon, a dit la mer; et la force de la mer a dit: Je n'ai point enfanté, je n'ai point mis au monde, je n'ai point nourri de fils, je n'ai point élevé de vierges.
Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
5 Or quand l'Égypte apprendra ces choses, elle sera saisie de douleur à cause de Tyr.
Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
6 Allez à Carthage, poussez des cris de douleur, vous qui habitez cette île.
Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
7 N'est-ce pas elle qui faisait votre orgueil depuis les premiers temps, avant d'avoir été livrée?
Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
8 Qui a résolu ces choses contre Tyr? Comment est-elle amoindrie? comment est-elle sans force? Ses marchands étaient renommés, c'étaient les princes de la terre.
Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
9 Le Seigneur a résolu d'abattre l'orgueil de tous ces glorieux, et d'humilier leur superbe sur la terre.
Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
10 Travaille maintenant à la terre; car il ne vient plus chez toi de vaisseaux de Carthage.
Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
11 Ta main ne prévaut plus sur la mer, cette main qui irritait les rois. Le Seigneur Dieu des armées a donné un ordre contre Chanaan pour que sa force fût détruite.
Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
12 Et l'on dira: Vous ne continuerez plus à outrager et à maltraiter la fille de Sidon. Et quand tu t'en iras chez les Citiens, tu n'y trouveras plus le repos,
Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
13 Ni dans la terre des Chaldéens; elle aussi a été désolée par les Assyriens, car son rempart est tombé.
Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
14 Poussez des cris de douleur, vaisseaux de Carthage, parce que votre force a péri.
Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
15 Et il arrivera ce jour-là que Tyr sera abandonnée durant soixante-dix ans, le temps que vit un homme, le temps que vit un roi; et après ces soixante-dix ans, Tyr chantera comme une courtisane.
A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
16 Prends la cithare, cours à l'aventure, ville prostituée, livrée à l'oubli; joue bien, chante beaucoup; pour qu'on se souvienne de toi.
“Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
17 Et après ces soixante-dix ans le Seigneur visitera Tyr, et il la rétablira comme autrefois, et elle sera un marché pour tous les royaumes qui couvrent la face de la terre;
A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
18 Et son commerce et ses revenus seront consacrés au Seigneur; et ce n'est point pour eux qu'ils amasseront, mais pour ceux qui résident devant le Seigneur; et tous ses gains seront employés à manger et à boire, et à se rassasier dans des banquets commémoratifs devant le Seigneur.
Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.

< Isaïe 23 >