< Isaïe 2 >

1 Parole qui vint à Isaïe, fils d'Amos, sur la Judée et sur Jérusalem.
Ga abin da Ishaya ɗan Amoz ya gani game da Yahuda da Urushalima.
2 Aux derniers jours la montagne du Seigneur sera glorieuse; sur la cime des monts apparaîtra la maison de Dieu; elle s'élèvera au-dessus des collines, et tous les Gentils y viendront.
A kwanaki masu zuwa za a kafa dutsen haikalin Ubangiji a matsayin babba cikin duwatsu; za a daga shi bisa tuddai, kuma dukan al’ummai za su bumbunto zuwa gare shi.
3 Et maintes nations partiront, disant: Allons et montons à la montagne du Seigneur et à la maison du Dieu de Jacob, et il nous annoncera sa voie, et nous y marcherons; car la loi sortira de Sion, et la parole du Seigneur, de Jérusalem.
Mutane da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, domin mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Dokar za tă fito daga Sihiyona, maganar Ubangiji daga Urushalima.
4 Et il jugera entre les nations, et il réprimandera nombre de peuples. Et de leurs glaives ils forgeront des charrues, et des faux de leurs javelines; et l'on ne tirera plus l'épée nation contre nation, et l'on n'apprendra plus à se faire la guerre.
Zai shari’anta tsakanin al’ummai zai kuma sulhunta faɗar mutane masu yawa. Za su mai da takubansu su zama garemani māsunsu su zama wuƙaƙen askin itatuwa. Al’umma ba za tă ƙara ɗauki takobi a kan al’umma ba, ba kuwa za su ƙara yin horarwar yaƙi.
5 Et maintenant venez, maison de Jacob, et marchons à la lumière du Seigneur.
Ki zo, ya gidan Yaƙub, bari mu yi tafiya a hasken Ubangiji.
6 Car il avait abandonné son peuple, la maison d'Israël; parce qu'au commencement leur terre était remplie de devins et d'augures, comme celle des Philistins, et que beaucoup d'enfants leur étaient nés de femmes étrangères
Ka rabu da mutanenka, gidan Yaƙub. Sun cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas; suna yin duba kamar Filistiyawa suna tafa hannuwa tare da marasa sanin Allah.
7 Leur terre regorgeait d'argent et d'or, et leurs trésors étaient sans nombre. Et leur pays était couvert de chevaux, et l'on ne pouvait compter leurs chars.
Ƙasarsu ta cika da azurfa da zinariya; dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu ta cika da dawakai; kekunan yaƙinsu kuma ba iyaka.
8 Et la terre était remplie de leurs œuvres d'abomination, faites de leurs mains, et ils adoraient des dieux façonnés de leurs doigts.
Ƙasarsu ta cika da gumaka; sukan rusuna ga aikin hannuwansu, ga abin da yatsotsinsu suka yi.
9 Et l'homme se courbait, et le guerrier s'humiliait; non, je ne leur pardonnerai point.
Saboda an jawo mutum ƙasa aka kuma ƙasƙantar da ɗan adam, kada ku gafarta musu.
10 Et maintenant entrez parmi les rochers, et cachez-vous dans la terre devant la crainte du Seigneur, devant sa gloire et sa puissance, lorsqu'il se lèvera pour frapper la terre.
Ku tafi cikin duwatsu, ku ɓuya cikin ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa!
11 Car les yeux du Seigneur sont en haut, et l'homme en bas. Et la hauteur des hommes sera abattue, et en ce jour le Seigneur seul sera élevé en gloire.
Za a ƙasƙantar da mai girman kai za a kuma lalatar da fariyar masu ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana.
12 Le jour du Seigneur des armées sera contre tout homme insolent et superbe, contre tout homme altier et orgueilleux, et ils seront abaissés.
Ubangiji Maɗaukaki yana da rana ajiye domin dukan masu girman kai da masu fariya domin dukan waɗanda aka ɗaukaka (zai kuwa ƙasƙantar da su),
13 Ce jour sera contre le grand cèdre du Liban qui s'élève jusqu'au ciel, et contre le palmier de Basan;
domin dukan al’ul na Lebanon, masu tsayi da masu fariya, da kuma dukan itatuwan oak na Bashan,
14 Contre les hautes montagnes et les hautes collines,
domin dukan dogayen duwatsu da kuma tuddai masu tsayi,
15 Contre les tours altières et les remparts altiers,
domin kowace doguwar hasumiya da kowace katanga mai ƙarfi,
16 Contre tous les vaisseaux de la mer, et contre les plus beaux navires.
domin kowane jirgin ruwan kasuwanci da kuma jirgi mafi girma mafi kyau.
17 Et tout homme sera humilié, et l'orgueil des hommes tombera, et en ce jour le Seigneur sera seul élevé en gloire.
Za a jawo mai girman kai ƙasa a kuma ƙasƙantar da mai ɗaga kai; Ubangiji kaɗai za a ɗaukaka a wannan rana,
18 Et ils cacheront toutes les idoles, œuvres de leurs mains,
za a kuma kawar da gumaka ƙaƙaf.
19 Les emportant dans les cavernes, dans les fentes des rochers, dans les profondeurs de la terre, devant la crainte du Seigneur, devant sa gloire et sa puissance, lorsqu'il se lèvera pour frapper la terre.
Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
20 Car ce jour-là l'homme rejettera les abominations d'or et d'argent qu'il aura faites pour adorer de vaines idoles et des oiseaux de nuit;
A wannan rana mutane za su zubar wa jaba da jamage gumakansu na azurfa da gumakansu na zinariya da suka yi don su bauta musu.
21 En pénétrant dans les creux, dans les cavernes et les fentes des plus durs rochers, devant la crainte du Seigneur, devant sa gloire et sa puissance, quand il se lèvera pour frapper la terre.
Za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma zuwa tsagaggun duwatsu daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?

< Isaïe 2 >