< Isaïe 10 >

1 Malheur à ceux qui écrivent l'iniquité! car en écrivant ainsi, c'est l'iniquité qu'ils gravent.
Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
2 Ils écartent du pauvre la justice, ils arrachent tout moyen de défense aux indigents de mon peuple, afin que la veuve soit pour eux un butin, l'orphelin une proie.
don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
3 Et que feront-ils au jour de la visite du Seigneur? car la tribulation viendra sur vous de loin. Vers qui vous réfugierez-vous pour avoir du secours? Et où cacherez-vous votre gloire,
Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
4 Pour n'être point entraînés en captivité? Sur vous tous s'est tournée la colère du Seigneur, et sa main est encore levée.
Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
5 Malheur aux Assyriens! la verge de mon courroux, ma colère est dans leurs mains.
“Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
6 J'enverrai ma colère contre une nation inique, et je commanderai à mon peuple de recueillir du butin et des dépouilles, de fouler aux pieds les villes et de les réduire en poussière.
Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
7 Mais lui, telle n'est point sa pensée, tel n'est point le sentiment de son âme. Il mettra son orgueil à exterminer de nombreuses nations.
Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
8 Et si elles lui disent: Toi seul es roi;
Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
9 Il répondra: En effet, n'ai-je point pris la contrée au-dessus de Babylone, et Chalane où une tour a été construite? N'ai-je point pris l'Arabie, et Damas, et Samarie?
‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
10 Comme je les ai prises, ainsi je prendrai tous les royaumes. Lamentez- vous, statues de Jérusalem et de Samarie!
Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
11 Comme j'ai traité Samarie et les dieux fabriqués de ses mains, je traiterai Jérusalem et ses idoles.
ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
12 Puis voici ce qui arrivera: quand le Seigneur aura achevé d'accomplir ce qu'il veut faire en la montagne de Sion et à Jérusalem, je visiterai ce cœur superbe, ce roi des Assyriens, et la gloire altière de ses yeux.
Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
13 Car il a dit: J'agirai dans ma force; et dans la sagesse de mon intelligence j'effacerai les bornes des nations, et je les dépouillerai de leur puissance.
Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
14 Et j'ébranlerai les villes habitées; et la terre entière, je la prendrai comme un nid dans ma main; et je l'enlèverai comme des œufs abandonnés; car nul ne peut m'échapper ou me contredire.
Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
15 Mais la cognée peut-elle se glorifier sans celui qui s'en sert pour abattre? La scie peut-elle s'enorgueillir sans celui qui la tire? Il faut bien que quelqu'un lève la verge ou le bâton; mais non.
Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
16 Le Seigneur des armées enverra contre ton honneur le déshonneur, et contre ta gloire il allumera un feu ardent.
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
17 Et la lumière d'Israël sera cette flamme; elle le sanctifiera avec un feu ardent, et dévorera la forêt comme une herbe sèche.
Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
18 En ce jour s'évanouiront montagnes, collines et forêts, et la lumière d'Israël dévorera tout, depuis l'âme jusqu'aux chairs. Et celui qui fuira sera comme un homme qui fuit une flamme ardente;
Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
19 Et ceux qui resteront seront en petit nombre, et un petit enfant pourra les compter.
Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
20 Et en ce jour voici ce qui arrivera: ce qui restera d'Israël, et ceux de Jacob qui auront été sauvés n'auront plus foi en ceux qui leur auront nui; mais ils se confieront en vérité à Dieu, au Saint d'Israël.
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
21 Et ce qui restera de Jacob se confiera au Dieu tout-puissant.
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
22 Et quand le peuple d'Israël serait aussi nombreux que le sable de la mer, un reste en sera seul sauvé.
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
23 Parole abrégée et accomplie avec justice; car cette parole abrégée, le Seigneur l'étendra à toute la terre.
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
24 A cause de cela, voici ce que dit le Seigneur des armées: Ne crains pas, ô mon peuple; habitants de Sion, ne craignez pas l'Assyrien; il te frappera avec une verge; car j'amènerai sur toi cette plaie, pour que tu y reconnaisses la voie d'Égypte.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
25 Encore un peu de temps, et ma colère s'apaisera; mais alors mon courroux se tournera contre les conseils de tes ennemis.
Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
26 Et le Seigneur suscitera contre eux une plaie semblable à celle de Madian dans le lieu de l'affliction; et son courroux éclatera comme autrefois contre l'Égypte sur le chemin de la mer Rouge.
Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
27 Et en ce jour voici ce qui arrivera: ton joug sera ôté de ton épaule, et tu seras délivré de ta crainte, et le joug qui pesait sur tes épaules sera réduit en poudre.
A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
28 Il marchera d'abord sur la ville d'Aggaï, passera par Maggédo et déposera à Machma ses appareils de guerre.
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
29 Puis il traversera la vallée et entrera dans Aggaï; la terreur saisira Rama, ville de Saul.
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
30 La fille de Gallim prendra la fuite; on l'apprendra à Lasa, on l'apprendra à Anathoth.
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
31 Et la stupeur a frappé Madebina, et les habitants de Gibbeïr.
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
32 Pour vous, consolez-vous aujourd'hui et restez fermes dans la voie; ô vous, collines de Jérusalem, consolez la montagne et Sion, ma fille.
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
33 Voilà que le maître, le Seigneur des armées, va de sa puissance confondre ces glorieux; et les grands seront brisés avec leur orgueil; et les superbes seront humiliés,
Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
34 Et les superbes périront car le glaive; et le Liban tombera avec ses cîmes.
Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.

< Isaïe 10 >