< Osée 2 >

1 Dites à votre frère, Mon-Peuple, et à votre sœur Pitié:
“Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
2 Plaidez contre votre mère; car elle n'est point Ma femme, et Je ne suis point son Mari. Et J'ôterai de devant Ma face sa prostitution, et son adultère du milieu de ses mamelles,
“Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
3 afin de la mettre nue, et de la remettre comme elle était le jour de sa naissance; et Je ferai d'elle un désert, et Je la traiterai comme une terre aride; et Je la tuerai par la soif;
In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
4 et Je n'aurai point pitié de ses enfants; car ce sont des enfants de prostitution.
Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
5 Leur mère s'est prostituée; celle qui les a portés les a couverts de honte; elle a dit: Je m'en irai après mes amants qui me donnent mon pain, et mon eau, et mes vêtements, et mon linge, et mon huile, et tout ce qui m'est nécessaire.
Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
6 C'est pourquoi Je ferme sa voie avec des épines, et Je bâtirai sur ses routes; elle ne retrouvera plus son sentier.
Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
7 Elle poursuivra ses amants, et ne les atteindra pas; elle les cherchera, et ne les trouvera pas; Et elle dira: Je vais partir, je vais retourner auprès de mon premier mari; car, pour moi, il faisait meilleur alors que maintenant.
Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
8 Et elle n'a point connu que Je lui avais donné du pain, du vin et de l'huile, et que Je l'avais comblée d'argent, et elle a fait à Baal des idoles d'argent et d'or.
Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
9 À cause de cela, Je M'en retournerai, Je prendrai Mon blé lors de la moisson, et Mon vin lors de la vendange; et Je reprendrai Mes vêtements et Mon linge, pour ne plus couvrir sa nudité.
“Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
10 Et désormais Je révélerai à ses amants son impureté, et nul ne la délivrera de Mes mains.
Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
11 Et Je supprimerai toutes ses joies, toutes ses fêtes, toutes ses nouvelles lunes, ses sabbats et toutes ses solennités.
Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
12 Et Je détruirai sa vigne et ses figuiers, parce qu'elle a dit: Ce sont les salaires que m'ont donné mes amants. Et Moi, J'en ferai un témoignage; les bêtes des champs viendront y paître, et les oiseaux du ciel, et les reptiles de la terre.
Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
13 Je lui ferai expier les jours où elle a sacrifié à Baal, et où elle a mis ses pendants d'oreilles et ses colliers pour s'en aller après son amant. Et elle M'a oublié, dit le Seigneur.
Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
14 C'est pourquoi Je l'égarerai et Je l'enverrai dans le désert, et je parlerai à son cœur.
“Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
15 Et de là Je lui rendrai ses possessions et la vallée d'Achor, pour lui ouvrir l'intelligence. Et là elle s'humiliera autant de jours qu'a duré sa jeunesse, et autant de jours qu'elle a mis à revenir de la terre d'Égypte.
A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
16 Et ceci arrivera en ce jour-là, dit le Seigneur; elle M'appellera Mon époux, et elle ne M'appellera plus Baal.
“A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
17 Et J'ôterai de sa bouche les noms de Baal, et l'on ne s'en souviendra plus.
Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
18 Et en ce jour-là J'établirai une alliance entre eux et les bêtes sauvages, et les oiseaux du ciel, et les reptiles de la terre; et Je briserai sur la terre l'arc, le glaive et les armes de guerre, et Je t'y installerai avec l'espérance.
A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
19 Et Je te prendrai pour épouse dans tous les siècles, et Je te prendrai pour épouse en Mon équité, en Mes jugements, en Ma pitié, en Ma miséricorde.
Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
20 Et Je te prendrai pour épouse avec confiance, et tu reconnaîtras le Seigneur.
Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
21 Et il arrivera en ce jour-là, dit le Seigneur, que J'exaucerai le ciel, et le ciel exaucera la terre.
“A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
22 Et la terre exaucera le blé, et le vin, et l'huile, et toutes ces choses exauceront Jezraël.
ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
23 Et Je la sèmerai pour moi sur la terre, et J'aimerai celle que Je n'aimais pas. Et Je dirai à Non-Mon-Peuple: Tu es Mon peuple; et il dira: Tu es le Seigneur mon Dieu.
Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”

< Osée 2 >