< Osée 14 >

1 Israël, reviens à ton Dieu; car tes fils s'énervent, à cause de tes iniquités.
Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
2 Prenez avec vous de bonnes paroles, et convertissez-vous au Seigneur votre Dieu: dites-Lui que vous renoncez aux récompenses de l'iniquité pour choisir le bien; dites-Lui: Nous T'offrons les fruits de nos lèvres!
Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
3 Assur ne nous sauvera pas; nous ne monterons plus à cheval; nous ne dirons plus aux œuvres de nos mains: Vous êtes nos dieux; Celui qui est en vous, Seigneur, aura pitié de l'orphelin!
Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
4 Le Seigneur a dit: Je restaurerai leurs demeures, Je les aimerai manifestement, parce qu'ils ont détourné d'eux Ma colère.
“Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
5 Je serai pour Israël comme la rosée; il fleurira comme le lis, et il jettera ses racines comme le cèdre du Liban.
Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
6 Ses rameaux s'étendront; il sera chargé de fruits comme un olivier, et il répandra ses parfum comme l'encens.
tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
7 Les peuples se convertiront et viendront s'asseoir sous son ombre; ils vivront et se rassasieront de son pain; et son mémorial fleurira comme une vigne, comme le vin du Liban
Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
8 en Éphraïm. Qu'y a-t-il encore de commun entre lui et les idoles? Je l'ai humilié, et Je rétablirai ses forces. Je suis comme un genièvre touffu; c'est de moi que viennent tes fruits.
Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
9 Qui est sage et comprendra ces choses? Qui est savant et les connaîtra? Les voies du Seigneur sont étroites; les justes y marchent, les impies y trébucheront.
Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.

< Osée 14 >