< Osée 12 >
1 Éphraïm a poursuivi un vent funeste qui a fait durer tout le jour l'ardente chaleur; il a multiplié les vanités et les folies; il a fait alliance avec les Assyriens; il a vendu de l'huile en Égypte.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 Et le Seigneur entrera en jugement avec Juda, afin de punir Jacob; et Il le rétribuera selon ses voies et ses œuvres.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 Dans les entrailles de sa mère, il supplanta son frère, et, de ses travaux, il fut fort contre Dieu.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 Il fut fort avec un ange, et il prévalut; et ils pleurèrent, et ils Me prièrent, ils Me trouvèrent en la maison d'On; et là il leur fut parlé.
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 Et le Seigneur Dieu Tout-Puissant sera le mémorial de Jacob.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Et toi, Éphraïm, tu te convertiras à ton Dieu; garde donc Sa miséricorde et Sa justice, et approche-toi toujours de ton Dieu.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 Chanaan tient dans sa main une balance d'iniquité; il a aimé à opprimer avec violence.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 Et Éphraïm a dit: Cependant je me suis enrichi, je me suis acquis le repos. Mais aucun de ses labeurs ne lui sera compté, à cause des injustices qu'il a commises.
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 Moi, le Seigneur ton Dieu, Je t'ai fait sortir de l'Égypte; Je te ferai encore camper sous des tentes, comme dans les jours de fête.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 J'ai parlé aux prophètes, et J'ai multiplié les visions, et J'ai parlé par la bouche des prophètes.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 Si Galaad n'est plus, c'est qu'il y avait en Galaad des princes menteurs faisant des sacrifices, et leurs autels sont comme des amas de pierres dans un champ.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 Et Jacob se retira en Syrie, et Israël servit pour une femme, et pour une femme il garda les troupeaux.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 Et par Son prophète le Seigneur conduisit Israël hors de la terre d'Égypte, et c'est encore par Son prophète qu'Il le sauva.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Et Éphraïm le provoqua et souleva Sa colère; mais le sang versé par Éphraïm retombera sur sa tête, et le Seigneur le rétribuera selon Son opprobre.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.