< Genèse 42 >
1 Or, Jacob, ayant vu qu'il y avait vente en Égypte, dit à ses fils: D'où vient votre nonchalance?
Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
2 Je sais qu'il y a du blé en Égypte; descendez-y et achetez-nous un peu de blé, afin que nous vivions et ne mourions pas.
Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
3 Et les dix frères de Joseph allèrent acheter du blé en Égypte.
Sai goma daga cikin’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
4 Mais Jacob n'envoya pas, avec ses frères, Benjamin, le frère de Joseph: Car, dit-il, j'ai peur qu'une maladie ne le prenne en chemin.
Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
5 Les fils de Jacob allèrent donc acheter, en compagnie de ceux qui partaient: car la famine était en la terre de Chanaan.
Sai’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
6 Or, Joseph était le chef de la contrée, et il vendait à tous les peuples de la terre; les frères de Joseph, étant arrivés, se prosternèrent devant lui, la face contre terre.
To, Yusuf ne gwamnar ƙasar wanda yake sayar da hatsi ga dukan mutanenta. Saboda haka sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka isa, sai suka rusuna masa har ƙasa da fuskokinsu.
7 À la vue de ses frères, Joseph les reconnut; mais il ne se fit point connaître à eux; il leur parla même avec sévérité, et il leur dit: D'où venez-vous? Et ils dirent: De la terre de Chanaan, acheter du blé.
Nan da nan da Yusuf ya ga’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
8 Joseph reconnaissait bien ses frères, mais ils ne le reconnaissaient point.
Ko da yake Yusuf ya gane’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.
9 Il se souvint alors des songes qu'il avait eus, et il leur dit: Vous êtes des espions; vous êtes venus épier ce qui se fait en la contrée.
Sa’an nan ya tuna da mafarkansa game da su, ya kuma ce musu, “Ku’yan leƙen asiri ne! Kun zo don ku leƙi asirin ƙasar ku ga inda ba ta da tsaro.”
10 Et ils dirent: Non, seigneur, tes serviteurs sont venus acheter des vivres.
Suka amsa suka ce, “A’a, ranka yă daɗe, bayinka sun zo don saya abinci ne.
11 Nous sommes tous fils d'un seul homme, nous sommes pacifiques, et tes serviteurs ne sont pas des espions.
Mu duka’ya’yan mutum ɗaya maza ne. Bayinka mutane ne masu gaskiya, ba’yan leƙen asiri ba ne.”
12 Non, reprit-il, vous êtes venus pour voir ce qui se fait en la contrée.
Ya ce musu “Sam! Kun zo ne ku ga inda ƙasarmu babu tsaro.”
13 Et ils dirent: Tes serviteurs étaient douze frères en la terre de Chanaan; le plus jeune, est aujourd'hui avec notre père, et l'autre ne vit plus.
Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne,’yan’uwa,’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
14 Joseph leur dit: C'est bien cela, c'est ce que je vous ai dit: vous êtes des espions;
Yusuf ya ce musu, “Daidai ne yadda na faɗa muku. Ku’yan leƙen asiri ne!
15 C'est par là que vous serez reconnus. Par la santé du Pharaon! vous ne sortirez pas d'ici que votre frère le plus jeune n'y soit venu.
Ga kuwa yadda za a gwada ku. Muddin Fir’auna yana a raye, ba za ku bar wannan wuri ba sai ƙaramin ɗan’uwanku ya zo nan.
16 Envoyez l'un de vous et qu'il amène votre frère; en attendant, vous allez être retenus jusqu'à ce que vos paroles soient confirmées, et que l'on sache si vous dites vrai ou non. Si vous avez menti, par la santé du Pharaon! vous êtes des espions.
Ku aiki ɗaya daga cikinku yă kawo ɗan’uwanku; za a sa sauranku a kurkuku, saboda a gwada maganarku a ga ko gaskiya ce kuke faɗi. In ba haka ba, to, da ran Fir’auna, ku’yan leƙen asiri ne!”
17 Et il les mit en prison trois jours.
Ya kuwa sa su duka a kurkuku na kwana uku.
18 Le troisième jour venu, il leur dit: Faites ce que je vais vous dire, et vous vivrez, car je crains Dieu.
A rana ta uku, Yusuf ya ce musu, “Ku yi wannan za ku kuwa rayu, gama ina tsoron Allah.
19 Si vous êtes pacifiques, que l'un de vous reste en prison, et que les autres partent; allez, emportez votre blé,
In ku mutane masu gaskiya ne, ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku yă zauna a kurkuku, yayinda sauranku su tafi, su kai hatsi don gidajenku da suke yunwa.
20 Et amenez-moi votre frère le plus jeune: ainsi vos paroles seront confirmées; si vous vous y refusez, apprêtez-vous à mourir. Et ils firent comme il avait dit.
Amma dole ku kawo ƙaramin ɗan’uwanku gare ni, saboda a tabbatar da maganarku har ba za ku mutu ba.” Suka kuwa yi haka.
21 Sur quoi, chacun dit à son frère: Oui, c'est mérité, car nous sommes coupables au sujet de notre frère; nous n'avons eu aucun souci de l'affliction de son âme; lorsqu'il nous suppliait, nous ne l'avons pas écouté; c'est pourquoi cette affliction est tombée sur nous.
Sai suka ce wa juna, “Tabbatacce ana hukunta mu ne saboda ɗan’uwanmu. Mun ga yadda ya yi wahala sa’ad da ya roƙe mu saboda ransa, amma ba mu saurare shi ba, shi ya sa wannan wahala ta zo mana.”
22 Ruben ajouta: Ne vous ai-je point dit: Ne maltraitez pas l'enfant? Mais vous n'avez rien voulu entendre, et voilà que son sang est vengé.
Ruben ya amsa, “Ban faɗa muku cewa kada ku ɗauki alhakin yaron nan ba, sai kuka ƙi ji, to, yau ga alhakin jininsa muke biya.”
23 Ils parlaient entre eux et ne savaient pas que Joseph les entendait, car il s'était servi avec eux d'un interprète.
Ba su san cewa Yusuf yana jin su ba, da yake yana amfani da mai fassara ne.
24 Et Joseph, s'étant éloigné, pleura; revenu auprès d'eux, il leur parla, prit Siméon, et l'enchaîna devant eux.
Sai ya juya daga gare su ya yi kuka, sa’an nan ya dawo ya yi musu magana kuma. Ya sa aka ɗauke Simeyon daga gare su, aka daure shi a idanunsu.
25 Cependant, Joseph ordonna qu'on remplit leurs sacs, que dans chacun on remît l'argent, et qu'on leur donnât des vivres pour la route; et il fut fait comme il avait dit.
Yusuf ya yi umarni a cika buhunansu da hatsi, a kuma sa azurfan kowane mutum a cikin buhunsa, a kuma ba su kalaci don tafiyarsu. Bayan aka yi musu wannan,
26 Après avoir chargé le blé sur leurs ânes, ils se mirent en route.
suka jibga hatsinsu a kan jakuna, sai suka kama hanya.
27 Or, l'un d'eux, ayant délié son sac pour faire manger les ânes à la première halte, vit, à l'entrée du sac, sa bourse d'argent.
A wurin da suka tsaya don su kwana, ɗaya daga cikinsu ya buɗe buhunsa don yă ciyar da jakinsa, sai ya ga azurfansa a bakin buhunsa.
28 Et il dit à ses frères: L'argent m'a été rendu, le voici dans mon sac; leur cœur fut saisi, ils se troublèrent; car ils se disaient les uns aux autres: Pourquoi Dieu nous a-t-il fait cela?
Sai ya ce wa’yan’uwansa, “An mayar mini da azurfata. Ga shi a cikin buhuna.” Zuciyarsu ta karai, suka dubi juna suna rawan jiki, suka ce, “Mene ne wannan da Allah ya yi mana?”
29 Arrivés chez Jacob, leur père, en la terre de Chanaan, ils lui racontèrent tout ce qui leur était advenu, disant:
Sa’ad da suka zo wurin mahaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana, suka faɗa masa dukan abin da ya faru da su. Suka ce,
30 L'homme maître de la contrée nous a parlé sévèrement, et il nous a emprisonnés comme espions.
“Mutumin da yake shugaba a ƙasar ya yi mana matsananciyar magana, ya kuma ɗauke mu tamƙar’yan leƙen asirin ƙasa.
31 Nous lui avons dit: Nous sommes pacifiques, nous ne sommes point des espions.
Amma muka ce masa, ‘Mu masu gaskiya ne; mu ba’yan leƙen asiri ba ne.
32 Nous étions douze frères, fils du même père; l'un ne vit plus, et le plus jeune est aujourd'hui avec notre père, en la terre de Chanaan.
Dā mu’yan’uwa ne goma sha biyu,’ya’yan mahaifi guda maza. Ɗayanmu ya rasu, kuma ƙaramin yanzu yana tare da mahaifinmu a Kan’ana.’
33 Mais l'homme maître de la contrée nous a dit: Vous me donnez vous-mêmes le moyen de savoir si vous n'êtes pas des espions, et si vous êtes pacifiques: laissez-moi l'un de vous, et, prenant les vivres que vous avez achetés pour votre maison, partez.
“Sai mutumin wanda yake shugaba a kan ƙasar ya ce mana, ‘Ga yadda zan san ko ku mutane masu gaskiya ne. Ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku a nan tare da ni, ku ɗauki abinci domin gidajenku masu yunwa, ku tafi.
34 Allez me chercher votre plus jeune frère: je connaîtrai alors que vous n'êtes point des espions, mais que vous êtes pacifiques; je vous rendrai votre frère, et vous pourrez négocier en ce pays.
Amma ku kawo mini ƙaramin ɗan’uwanku domin in san cewa ku ba’yan leƙen asiri ba ne, amma mutane ne masu gaskiya. Sa’an nan zan mayar muku da ɗan’uwanku, ku kuma iya yin sana’a a ƙasar.’”
35 Or, lorsqu'ils vidèrent leurs sacs, chacun trouva dans son sac sa bourse d'argent; ils virent les bourses d'argent, leur père les vit aussi, et ils eurent crainte.
Yayinda suke juyewa hatsi daga buhunansu, sai ga ƙunshin azurfan kowane mutum a buhunsa! Sa’ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshe-ƙunshen kuɗi, suka firgita.
36 Sur quoi Jacob, leur père, s'écria: Vous m'avez privé de mes enfants. Joseph n'est plus; Siméon n'est plus; me prendrez-vous aussi Benjamin? C'est sur moi que tout tombe.
Yaƙub mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashin’ya’yana. Yusuf ya rasu, Simeyon kuma ba ya nan, yanzu kuma kuna so ku ɗauki Benyamin. Kome yana gāba da ni!”
37 Ruben répondit à son père: Fais mourir mes deux fils si je ne te ramène le tien; remets-le entre mes mains, et je le reconduirai près de toi.
Sai Ruben ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe dukan’ya’yana maza, in ban dawo da shi gare ka ba. Ka sa shi ga kulawata, zan kuwa dawo da shi.”
38 Mais Jacob dit: Mon fils ne partira pas avec vous; son frère est mort, celui-ci seul m'est resté; une maladie le prendra dans le chemin où vous irez, et, de tristesse, vous ferez descendre ma vieillesse au sein de la terre. (Sheol )
Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol )