< Genèse 35 >

1 Dieu dit ensuite à Jacob: Lève-toi, pars pour Béthel, établis là ta demeure et élève en ce lieu un autel au Dieu qui t'y est apparu, lorsque tu fuyais Esaü ton frère.
Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
2 Jacob alors dit aux siens et à tous ceux qui étaient avec lui: Faites disparaître du milieu de vous les dieux étrangers qui s'y trouvent; purifiez- vous et changez de vêtement.
Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
3 Puis, levons-nous, allons à Béthel; nous y bâtirons un autel au Dieu qui m'a exaucé en un jour d'affliction, à celui qui fut avec moi, et qui m'a sauvé dans la voie où je marchais.
Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
4 Ils donnèrent donc à Jacob les dieux étrangers qui étaient entre leurs mains, ainsi que les pendants d'oreilles. Jacob les enfouit sous le térébinthe des Sécimes, et on ne les a jamais retrouvés jusqu'à ce jour.
Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
5 Israël décampa de la terre des Sécimes, et une terreur causée par Dieu tomba sur toutes les villes des alentours, en sorte que les fils de Jacob ne furent point poursuivis.
Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
6 Et Jacob ainsi que tout le peuple qui étais avec lui arrivèrent à Luza, la même que Béthel, en la terre de Chanaan.
Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
7 Il y bâtit un autel, et il donna à ce lieu le nom de Béthel, parce que c'est là que le Seigneur lui était paru, quand il fuyait Esaü son frère.
A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
8 Cependant Déborra, la nourrice de Rachel, mourut, et elle fut ensevelie sous un chêne au-dessous de Béthel, et Jacob nomma l'arbre Chêne de deuil.
To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
9 Or, Dieu apparut encore à Jacob en Luza, à son retour de la Mésopotamie Syrienne, et Dieu le bénit,
Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
10 Et lui dit: Tu ne t'appelleras plus Jacob, mais ton nom sera Israël. Et il s'appela Israël.
Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
11 Dieu lui dit: Je suis ton Dieu: crois et multiplie; des nations et des réunions de nations proviendront de toi, et des rois sortiront de tes reins.
Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
12 La terre que j'ai donnée à Abraham et Isaac, je te la donne; elle sera à toi, et après toi je donnerai cette terre à ta race.
Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
13 Après quoi, Dieu s'éloigna de lui et du lieu où il avait parlé.
Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14 Aussitôt, Jacob, au lieu même où Dieu lui avait parlé, dressa une colonne de pierre sur laquelle il répandit des libations et versa de l'huile.
Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
15 Et il nomma Béthel le lieu où Dieu lui avait parlé.
Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
16 Ensuite ayant décampé de Béthel, Jacob, dressa ses tentes au delà de la tour de Gader. Comme il approchait de Habrath pour arriver en Éphratha, Rachel enfanta, et elle souffrit beaucoup dans l'enfantement.
Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
17 Il advint, pendant qu'elle enfantait ainsi péniblement, que la sage-femme lui dit: Prends courage, c'est un fils.
Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
18 Or, au moment où son âme allait la quitter, car elle mourut, elle lui donna le nom de Fils de ma douleur (Bénoni), mais le père l'appela Benjamin.
Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
19 Rachel mourut donc et fut ensevelie sur le chemin de l'hippodrome d'Éphratha, aujourd'hui Bethléem.
Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
20 Et Jacob dressa sur son sépulcre une colonne qu'on nomme encore aujourd'hui: Colonne du sépulcre de Rachel.
Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
22 Or, tandis qu'Israël demeurait en cette terre, Ruben s'éloigna et dormit avec Balla, concubine de son père Jacob. Israël apprit le fait et l'eut en abomination. Or, les fils de Jacob étaient douze.
Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
23 Fils de Lia: premier-né de Jacob, Ruben, puis Siméon, Lévi, Issachar et Zabulon;
’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
24 Fils de Rachel, Joseph et Benjamin
’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
25 Fils de Balla, servante de Rachel, Dan et Nephthali;
’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
26 Fils de Zelpha, servante de Lia, Gad et Aser: tels sont les fils de Jacob qui lui naquirent en la Mésopotamie Syrienne.
’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
27 Jacob alla ensuite en Membré, auprès d'Isaac son père, dans la ville de la plaine qui est Hébron, en la terre de Chanaan, où Abraham et Isaac furent passagers.
Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
28 Bientôt les jours que vécut Isaac formèrent cent-quatre-vingts ans.
Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
29 Isaac mourut, et il se réunit à son peuple, âgé et plein de jours; ses fils Esaü et Jacob l'ensevelirent.
sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.

< Genèse 35 >