< Esdras 6 >

1 Alors, le roi Darius fit un édit pour que l'on cherchât dans les bibliothèques où est le trésor de Babylone.
Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
2 Et l'on trouva en cette ville, dans le palais, un chapitre où ce mémorial était écrit.
Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
3 En la première année de la domination du roi Cyrus, le roi Cyrus a fait cet édit, touchant le saint temple de Dieu à Jérusalem: Que le temple soit rebâti, ainsi que le lieu où l'on sacrifiait des victimes. Et il en a déterminé la hauteur et la largeur: soixante coudées des deux parts.
A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
4 Et il a ajouté: Qu'il y ait trois étages en pierres dures et un en bois, et que la dépense soit supportée par le trésor royal.
Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
5 Que l'on rende les vases d'or et d'argent du temple de Dieu, apportés de Jérusalem par Nabuchodonosor, et mis à Babylone; qu'ils retournent au temple de Jérusalem, à la place où ils étaient, dans le temple de Dieu.
Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
6 Maintenant, vous, gouverneurs au delà du fleuve, vous, Satharbuzanaï et Apharsachéens, mes serviteurs au delà du fleuve, donnez-leur ces choses, et tenez-vous loin d'eux.
Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
7 Laissez faire les travaux du temple de Dieu: que les chefs des Juifs, que leurs anciens bâtissent le temple au lieu où il était.
Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
8 Un édit est aussi rendu par moi pour que vous ne vous mêliez en rien de ce que feront les anciens des Juifs, pendant qu'ils bâtiront le temple de ce Dieu, et que, dans le but de ne point arrêter les travaux, on donne avec zèle à ces hommes, sur les impôts du roi, levés au delà de l'Euphrate, ce qu'il faudra pour la dépense.
Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
9 Et, ce qui viendrait à leur manquer, qu'on le leur donne jour par jour, à mesure qu'ils le demanderont, soit des bœufs, des béliers, des agneaux, pour les holocaustes du Dieu du ciel, soit du froment, du sel, du vin et de l'huile, selon le besoin des prêtres qui se trouvent à Jérusalem,
A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
10 Afin qu'ils fassent aisément leurs offrandes d'odeur de suavité au Dieu du ciel, et qu'ils prient pour la vie du roi et de ses fils.
domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
11 Et j'ai fait un édit portant que quiconque s'écartera de mes ordres sera attaché à une poutre enlevée de sa maison, et mis à mort sur ce bois, et que sa maison sera confisquée.
Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
12 Puisse le Dieu, dont le nom résidera en ce temple, renverser tout roi ou peuple qui étendra la main pour endommager ou détruire le temple de Dieu à Jérusalem. Moi, Darius, j'ai fait cet édit; qu'on soit attentif à s'y conformer.
Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
13 Alors, Tanthanaï, gouverneur en deçà de l'Euphrate; Satharbuzanaï, et les autres serviteurs du roi à qui Darius avait écrit, lui obéirent avec zèle.
Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
14 Et les anciens des Juifs et les lévites bâtirent, selon la prophétie d'Aggée le prophète, et de Zacharie, fils d'Addo; et ils bâtirent, et ils achevèrent le temple suivant la volonté de Dieu, et grâce aux édits de Cyrus, de Darius et d'Arthasastha, rois des Perses.
Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
15 Et ils achevèrent le temple le troisième jour du mois d'adar, et la sixième année du règne de Darius.
An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
16 Et les fils d'Israël, et les prêtres, et les lévites, et le reste des fils de l'exil, firent, avec allégresse, la dédicace du temple de Dieu.
Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
17 Pour la dédicace du temple de Dieu, ils offrirent cent bœufs, deux cents béliers, quatre cents agneaux; et l'offrande pour les péchés de tout Israël fut de douze boucs, nombre égal à celui des tribus d'Israël.
Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
18 Ils rétablirent les prêtres selon leurs divisions, et les lévites selon leurs catégories, pour le service de Dieu à Jérusalem, comme il est écrit au livre de Moïse.
Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
19 Et les fils de l'exil firent la Pâque le quatorzième jour du second mois.
A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
20 Car les prêtres et les lévites s'étaient purifiés; ils avaient tous été reconnus purs. Et ils immolèrent la pâque pour tous les fils de l'exil, et pour leurs frères les prêtres et les lévites.
Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
21 Et les fils d'Israël mangèrent la pâque, tant ceux qui étaient revenus de l'exil que ceux qui s'étaient préservés de l'impureté des peuples de la contrée, leurs voisins, et qui avaient cherché le Seigneur Dieu d'Israël.
Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
22 Et ils célébrèrent la fête des Azymes durant sept jours avec allégresse; car le Seigneur les réjouit, et il avait incliné le cœur du roi d'Assyrie en leur faveur pour fortifier leurs mains dans les travaux du temple du Dieu d'Israël.
Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.

< Esdras 6 >