< Esdras 4 >

1 Et ceux qui opprimaient Juda et Benjamin ouïrent que les enfants de la captivité bâtissaient un temple au Seigneur Dieu d'Israël.
Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
2 Et ils s'approchèrent de Zorobabel et des chefs de famille, et ils leur dirent: Nous bâtirons avec vous, parce que, comme vous, nous cherchons notre Dieu, et que nous lui sacrifions, depuis le temps d'Asaradan, roi des Assyriens, qui nous a transportés ici.
sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
3 Et Zorobabel, et Josué, et le reste des chefs de famille d'Israël, leur répondirent: Ce n'est pas avec vous que nous bâtirons un temple à notre Dieu; car, nous seuls, tous ensemble, nous bâtirons au Seigneur notre Dieu, comme nous l'a prescrit Cyrus, roi des Perses.
Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
4 Et le peuple de la terre affaiblissait les mains de Juda, et il l'empêchait de bâtir.
Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
5 Et des gens, salariés pour nuire aux fils de Juda, complotèrent pour ruiner leurs desseins, tant que vécut Cyrus, jusqu'au règne de Darius, roi des Perses.
Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
6 Au commencement du règne d'Assuérus, ils écrivirent une lettre contre ceux qui habitaient Jérusalem et Juda.
A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
7 Et, durant les jours d'Arthasastha, Tabéel écrivit une lettre bienveillante à Mithradate et aux autres serviteurs; le collecteur des impôts écrivit à Arthasastha, roi des Perses, une lettre en syriaque avec la traduction.
A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
8 Rheum le chancelier, et Samsa le scribe, écrivirent aussi une lettre contre Jérusalem au roi Arthasastha.
Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
9 Voici ce que jugent Rhéum le chancelier, Samsa le scribe, et le reste de ceux qui, avec nous, sont tes serviteurs: les Dinéens, les Apharsathachéens, les Tharphaléens, les Apharséens, les Arechyéens, les Babyloniens, les Susanachéens, les Davéens,
Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
10 Et les autres nations que le grand et vénérable Assenaphar a transportées dans les villes de Samarie; celles qui résident sur le territoire en deçà du fleuve.
da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
11 Suit la teneur de la lettre qu'ils envoyèrent: À Arthasastha, roi, ses serviteurs, en deçà du fleuve:
(Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
12 Que le roi sache que les Juifs qui sont partis de son territoire pour cette terre sont arrivés à Jérusalem, ville rebelle et méchante, qu'ils la rebâtissent, qu'ils en ont restauré les remparts, et qu'ils les ont élevés au-dessus des fondations.
Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
13 Que le roi sache bien qu'aussitôt leur ville reconstruite et leurs murs réparés, ils cesseront d'être tes tributaires, ils ne donneront rien; et ainsi, ils feront tort aux rois;
Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
14 Et il ne nous est point possible de voir le roi outragé; c'est pourquoi nous avons envoyé un message pour instruire le roi,
Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
15 Afin que l'on regarde dans le livre des archives de tes pères, où tu trouveras et tu apprendras que cette ville est une ville rebelle, qu'elle fait tort aux rois et aux royaumes, qu'il y a toujours eu chez elle des esclaves fugitifs, et que c'est pour cela qu'elle a été dépeuplée.
domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
16 Nous déclarons donc au roi que, si cette ville est rebâtie, si ses remparts sont relevés, il n'y aura plus de paix pour toi.
Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
17 Et le roi envoya dire à Rhéum le chancelier, à Samsa le scribe, et à ses serviteurs qui habitaient en Samarie et en deçà du fleuve: La paix;
Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
18 Le collecteur des impôts que vous nous avez envoyé a été appelé devant moi.
An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
19 Et j'ai fait un édit; puis, nous avons examiné, et nous avons trouvé que cette ville de tout temps s'est soulevée contre les rois; que la rébellion, que la désertion y résident.
Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
20 Or, il y a eu en Jérusalem des rois puissants; ils ont maîtrisé toute la contrée au delà de l'Euphrate; d'abondants revenus et des impôts leur ont été payés.
Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
21 Maintenant donc, faites un édit pour suspendre le travail de ces hommes; cette ville ne sera plus rebâtie.
Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
22 Soyez attentifs à maintenir cet édit; ne vous en relâchez point, de peur qu'un jour le mal ne s'y aggrave au détriment du roi.
Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
23 Le collecteur des impôts d'Arthasastha, roi, lut donc cette lettre devant Rhéum le chancelier, Samsa le scribe, et les autres serviteurs du roi, et ils allèrent en toute hâte à Jérusalem et en Juda avec des troupes et de la cavalerie, et ils arrêtèrent les travaux du peuple.
Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
24 Ainsi, la reconstruction du temple de Dieu fut suspendue à Jérusalem, et on ne la reprit qu'à la seconde année du règne de Darius.
Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.

< Esdras 4 >