< Ézéchiel 39 >

1 Et toi, fils de l'homme, prophétise maintenant contre Gog, et dis: Ainsi parle le Seigneur: Voilà que je suis contre toi, Gog, prince de Rhos, de Mésoch et de Thubal.
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
2 Je réunirai tes troupes, et je te guiderai; je te ferai partir des régions les plus lointaines de l'aquilon, et je te conduirai sur les montagnes d'Israël.
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
3 Et alors je briserai ton arc dans ta main gauche, et tes flèches dans ta main droite, et je te renverserai
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
4 Sur les montagnes d'Israël; et tu tomberas, toi et ceux qui t'appartiennent; et les nations qui t'accompagnent seront données à la multitude des oiseaux; et je t'ai donné toi-même à tous les oiseaux et à toutes les bêtes fauves des champs pour qu'ils te dévorent.
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
5 Tu tomberas sur la face de la terre; car moi j'ai parlé, dit le Seigneur.
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 Puis je lancerai la flamme sur Gog et sur les îles qui demeuraient en paix, et elles sauront que je suis le Seigneur.
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
7 Et mon saint nom sera connu au milieu de mon peuple d'Israël, et ils ne profaneront plus mon saint nom, et les nations sauront que je suis le Seigneur saint en Israël.
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
8 Voilà que le jour est venu, et l'on saura qu'il est venu, dit le Seigneur; le voilà le jour dont j'avais parlé.
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
9 Les habitants des villes en sortiront, et ils se chaufferont en brillant les armes, les boucliers, les épieux, les arcs, les flèches, les bâtons et les javelines; et ils en allumeront leur feu pendant sept ans.
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
10 Et ils ne prendront plus de bois dans les champs, et ils n'abattront plus d'arbres dans les forêts; mais ils feront du feu avec les armes, et ils pilleront ceux qui les ont pillés, et ils dépouilleront ceux qui les ont dépouillés, dit le Seigneur.
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
11 Et ceci adviendra: en ce jour-là je donnerai à Gog une place de renom, un sépulcre en Israël; ce sera le cimetière des voyageurs du côté de la mer, et l'on entourera de murs l'entrée de la vallée. Là on enterrera Gog et toute sa multitude, et ou l'appellera le cimetière de Gog.
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
12 Et la maison d'Israël les y enterrera, afin qu'en sept mois la terre soit purifiée;
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
13 Et tout le peuple de la terre les y enterrera; et ce sera pour eux une place de renom, le jour où Israël sera glorifié, dit le Seigneur.
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
14 Et ils ne cesseront pas d'envoyer des hommes qui parcourront la contrée pour ensevelir ceux qui seraient restés sur la face de la terre, et la purifier en sept mois; et ces hommes chercheront avec soin.
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
15 Et chacun de ceux qui parcourront la terre, à la vue d'un ossement humain, placera auprès une marque, afin que les fossoyeurs l'enterrent dans la vallée, au cimetière de Gog.
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
16 Car le nom de la vallée sera Cimetière; et la terre sera purifiée.
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
17 Et toi, fils de l'homme, dis: Ainsi parle le Seigneur: Dis à tout oiseau du ciel et à toute bête des champs: Rassemblez-vous, et partez; réunissez-vous de tous les alentours pour mon sacrifice, que je vous ai préparé, grand sacrifice sur les montagnes d'Israël; et mangez-en les chairs, et buvez-en le sang.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
18 Mangez les chairs des géants; buvez le sang des princes de la terre; mangez des béliers, des bœufs, des boucs et des bœufs, tous bien engraissés.
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
19 Mangez de la chair à satiété; buvez du sang jusqu'à l'ivresse; c'est la chair et le sang de mon sacrifice, que je vous ai préparé.
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
20 Et vous serez rassasiés à ma table de la chair du cavalier et du cheval, du géant et de tout guerrier, dit le Seigneur.
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Et je mettrai en vous ma gloire, et toutes les nations verront mon jugement que j'aurai exécuté, et ma main que j'aurai portée sur eux.
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
22 Et la maison d'Israël saura de ce jour-là et pour tous les temps que je suis le Seigneur leur Dieu.
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
23 Et les nations sauront que la maison d'Israël a été captive à cause de ses péchés, et qu'en punition de ce qu'elle m'a répudié, j'ai détourné d'elle mon visage; que je l'ai livrée à ses ennemis, et qu'elle est tombée sous le glaive.
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
24 Je les ai traités selon leurs impuretés et leurs égarements, et j'ai détourné d'eux mon visage.
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
25 C'est pourquoi voici ce que dit le Seigneur Maître: Maintenant je ramènerai les captifs en Jacob, et je ferai miséricorde à la maison d'Israël, et je serai jaloux pour l'amour de mon saint nom.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
26 Et ils subiront leur déshonneur et l'iniquité qu'ils ont commise quand ils habitèrent leur terre en paix; et nul ne les épouvantera,
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
27 Lorsque je les aurai retirés d'entre les nations et réunis de toutes les contrées des gentils; et en présence des nations je serai sanctifié parmi eux.
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
28 Et ils sauront que je suis le Seigneur leur Dieu, quand je me serai manifesté à eux en présence des nations.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
29 Et je ne détournerai plus d'eux mon visage, parce que j'aurai assouvi ma colère contre la maison d'Israël, dit le Seigneur Maître.
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 39 >