< Ézéchiel 25 >

1 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, tourne ta face contre les fils d'Ammon, et prophétise contre eux.
“Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
3 Et dis aux fils d'Ammon: Écoutez la parole du Seigneur; ainsi parle le Seigneur: En punition de ce que vous vous êtes réjouis contre mes choses saintes, parce qu'elles ont été profanées, et contre Israël, parce qu'il a été détruit, et contre la maison de Juda, parce qu'elle a été emmenée en captivité;
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
4 En punition de cela, je vous livre en héritage aux fils de Cédem, et ils séjourneront chez toi, avec leurs bagages, et ils y dresseront leurs tentes; ils mangeront tes fruits et ils boiront ton lait.
saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
5 Et je ferai de la ville d'Ammon un pâturage pour leurs chameaux, et des fils d'Ammon un pâturage pour leurs brebis, et vous saurez que je suis le Seigneur.
Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
6 Car voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que tu as battu des mains et frappé du pied, et de ce que tu t'es réjoui en ton âme contre la terre d'Israël,
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
7 En punition de cela, j'étendrai sur toi ma main, et je te livrerai en proie aux nations, et je te détruirai parmi les peuples, et je t'anéantirai, et tu sauras que je suis le Seigneur.
saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
8 Voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que Moab a dit: La maison d'Israël n'est-elle point maintenant comme toutes les nations?
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
9 En punition de cela, voilà que je vais briser l'épaule de Moab, loin de ses villes frontières, sa terre choisie, la maison de Béthasimuth, située sur la fontaine de la ville maritime.
saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
10 J'ai envoyé les fils de Cédem contre les fils d'Ammon, pour qu'ils en fassent leur héritage, et qu'il ne reste plus de souvenir des fils d'Ammon:
Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
11 Et je tirerai aussi vengeance de Moab, et ils sauront que je suis le Seigneur.
zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
12 Voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce qu'a fait l'Idumée, qui, en châtiant la maison de Juda, s'est souvenue de sa propre haine, et s'est elle-même vengée;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
13 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: J'étendrai aussi la main sur l'Idumée, et j'y exterminerai les hommes et le bétail, et j'en ferai un désert; et ceux de Théman que l'on poursuivra tomberont sous le glaive.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
14 Et je punirai l'Idumée par les mains de mon peuple d'Israël, et ils traiteront l'Idumée selon ma colère et ma fureur, et ils connaîtront ma vengeance, dit le Seigneur.
Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que les Philistins, en châtiant mon peuple, ont fait revivre leur propre vengeance, et se sont enorgueillis en leur âme de les faire périr jusqu'au dernier;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
16 À cause de cela, ainsi dit le Seigneur: Voilà que j'étendrai ma main sur les étrangers, et j'exterminerai les Crétois, et je détruirai le reste des habitants de la côte.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
17 Et je les frapperai de mes grandes vengeances, et ils sauront que je suis le Seigneur, quand ma vengeance tombera sur eux.
Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”

< Ézéchiel 25 >