< Ézéchiel 23 >

1 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, il y avait deux femmes, filles d'une seule mère.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 Et dans leur jeunesse, elles se sont prostituées en Égypte; c'est là que leurs mamelles sont tombées et qu'elles ont été déflorées de leur virginité.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Et elles s'appelaient: l'aînée Oola; sa sœur Ooliba. Et elles ont été à moi, et elles ont enfanté des fils et des filles, et voici leurs vrais noms: Samarie était Oola, et Jérusalem était Ooliba.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 Et Oola me quitta pour se prostituer; elle aima jusqu'à la fureur ses amants les Assyriens, qui demeuraient auprès d'elle,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 Vêtus d'hyacinthe, princes et capitaines, jeunes gens d'élite, tous cavaliers montant à cheval.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 Et c'est à eux qu'elle se livra dans sa débauche, et tous les fils choisis des Assyriens, et tous ceux qu'elle aima si furieusement, la souillèrent au gré de tous leurs désirs.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Et elle ne renonça pas à sa débauche de l'Égypte; car c'est là que des hommes avaient dormi avec elle dans sa jeunesse, et ils l'avaient déflorée, et ils avaient versé sur elle leur propre infamie.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 À cause de cela, je l'ai livrée aux mains de ses amants, aux mains des fils des Assyriens qu'elle a aimés avec fureur.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Ils ont dévoilé sa honte; ils ont pris ses fils et ses filles; et ils l'ont tuée elle-même à coups de glaive. Et elle est devenue la fable des femmes, et ils ont tiré vengeance d'elle sur sa fille.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 Et sa sœur Ooliba la vit; et en ses passions elle fut plus dépravée qu'elle, et en sa prostitution elle surpassa la prostitution de sa sœur.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Elle aima avec fureur les fils des Assyriens, princes et capitaines, ses voisins, revêtus d'habits brodés, cavaliers montant à cheval, tous jeunes gens d'élite.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 Et je les vis toutes deux marcher dans les mêmes souillures.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 Et Ooliba alla plus loin dans sa débauche; elle vit des hommes dessinés sur un mur, images de Chaldéens tracés au pinceau,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 Les reins ceints d'étoffes bigarrées, la tête couverte d'étoffes de couleur, trois fois plus grands que les autres hommes, images de fils des Chaldéens, de la terre de leurs aïeux.
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 Et les ayant contemplés de ses yeux, elle les aima avec fureur, et elle leur envoya des messagers en la terre des Chaldéens.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 Et les fils de Babylone vinrent à elle; ils partagèrent sa couche; ils la souillèrent en sa prostitution, et elle fut souillée par eux; puis son âme s'éloigna d'eux.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Et elle dévoila sa débauche, et elle dévoila sa honte. Et mon âme s'éloigna d'elle comme mon âme s'était éloignée de sa sœur.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 Et tu as multiplié tes débauches, comme pour rappeler le souvenir des jours de ta jeunesse, où tu t'es prostituée en Égypte.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 Et tu as aimé avec fureur les Chaldéens, qui avaient des chairs comme des ânes, et des membres comme des chevaux.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 Et tu as renouvelé le dérèglement de ta jeunesse, et ce que tu as fait durant ton séjour en Égypte quand tu avais les mamelles de ta jeunesse.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 À cause de cela, Ooliba, voici ce que dit le Seigneur: Voilà que je vais susciter contre toi tes amants, de qui ton âme s'est éloignée; je les rassemblerai en cercle contre toi.
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 Les fils de Babylone et tous les Chaldéens, Phacuc, et Sué, et Hychué, et avec eux tous les fils des Assyriens, jeunes gens d'élite, princes et capitaines, tous ayant grand air et grand renom, cavaliers montant à cheval.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 Et ils viendront tous contre toi du nord, chars et roues, avec une multitude de peuples, longs boucliers, écus légers; et ils poseront autour de toi des gardes.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 Et je rendrai mon arrêt devant eux, et ils te puniront selon leurs lois. Et j'amènerai contre toi ma jalousie; et ils te traiteront avec des transports de colère. Ils te couperont les narines et les oreilles; ils frapperont du glaive ceux des tiens qui survivront; ils prendront tes fils et tes filles, et le feu dévorera ce qui restera de toi.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 Et ils te dépouilleront de tes vêtements, et ils te prendront les joyaux qui faisaient ton orgueil.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 Puis je détournerai de toi tes impiétés, et tes débauches de la terre d'Égypte, et tu ne lèveras plus les yeux sur eux, et tu ne te souviendras plus de l'Égypte.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 Ainsi parle-encore le Seigneur Maître: Voilà que je te livre aux mains de ceux que tu hais, de ceux de qui ton âme s'est éloignée.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 Ils te traiteront avec haine, et ils te prendront le fruit de tes fatigues et de tes labeurs, et tu seras nue et confuse; et la honte de ta prostitution sera dévoilée; et ton impiété et ta débauche
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 T'auront attiré ces maux, parce que tu t'es prostituée en courant après des gentils, et que tu t'es souillée avec leurs idoles.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Tu as marché dans la voie de ta sœur, et je mettrai sa coupe en tes mains.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 Voici ce que dit le Seigneur: Bois la coupe de ta sœur, coupe large et profonde; bois-la jusqu'à l'ivresse;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Et tu seras tout à fait énervée; la coupe de ta sœur Samarie est une coupe d'extermination.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 Bois-la, et je répudierai tes fêtes et tes jours de nouvelle lune; car c'est moi qui ai parlé, dit le Seigneur.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Parce que tu m'as oublié et rejeté derrière toi, tu recevras la rétribution de ton impiété et de ta débauche.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 Et le Seigneur me dit: Fils de l'homme, ne jugeras-tu pas Oola et Ooliba? Ne leur feras-tu pas connaître leurs dérèglements,
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Et leurs adultères, et le sang qu'elles ont versé? Elles se sont prostituées à leurs idoles; et leurs enfants qu'elles avaient enfantés pour moi, elles les ont fait passer pour elles à travers la flamme.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Et aussi longtemps qu'elles ont ainsi fait, elles ont souillé mes choses saintes et profané mes sabbats.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 Et quand elles égorgeaient leurs enfants pour des idoles, elles entraient dans mon sanctuaire pour le souiller; et voilà ce qu'elles ont fait au milieu de mon temple,
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 Avec des hommes venant de loin, à qui elles avaient envoyé des messages. Et comme ils arrivaient tu t'es aussitôt lavée, tu t'es fardée autour des yeux, tu t'es parée de tes joyaux,
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 Tu t'es assise sur un long siège, et une table était préparée devant toi; et ils se sont réjouis de mes parfums et de mon huile.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 Et elles ont entonné des chants harmonieux devant quelques-uns des hommes qui étaient venus en foule du désert, et elles leur ont mis des bracelets, et elles leur ont posé sur la tête des couronnes de gloire.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Et j'ai dit: Ne commettent-elles pas des adultères avec ceux-ci? Cette femme ne se conduit-elle pas comme une prostituée?
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 Ils sont entrés chez elle comme on entre chez une femme débauchée; et voilà comme ils sont entrés chez Oola et Ooliba, pour s'abandonner au dérèglement.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Aussi ce sont des hommes justes, ceux qui tireront vengeance contre ces femmes, de leurs adultères et du sang versé; car elles sont adultères et elles ont versé le sang.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 Voici ce que dit le Seigneur Maître: Ameute contre elles la foule, et répands chez elles le trouble et le pillage.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 Qu'elles soient lapidées par les pierres de la multitude, qu'elles soient percées par ses glaives; on tuera leurs fils et leurs filles, on brûlera leurs maisons.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 Ensuite je détournerai de cette terre l'impiété, et toutes les femmes seront instruites, elles n'imiteront pas l'impiété de celles-ci.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 Et votre iniquité retombera sur vous, et vous porterez la peine de vos idoles, et vous connaîtrez que je suis le Seigneur.
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 23 >