< Ézéchiel 22 >
1 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Et toi, fils de l'homme, ne jugeras-tu pas une ville de sang?
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Montre-lui toutes ses iniquités, et dis-lui: Ainsi parle le Seigneur Maître: Malheur à toi, ville, qui dans ton sein verses le sang pour que ton temps arrive, et qui t'es forgé des idoles pour te souiller
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Du sang de tes enfants que tu as répandu! Tu es tombée et tu t'es souillée, en te forgeant des idoles; tu as avancé tes jours, et hâté le temps de tes années. À cause de cela, je t'ai livrée aux outrages des gentils; et on fera de toi un sujet de raillerie en tous les royaumes
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Qui t'avoisinent, et en ceux qui sont loin de toi; et l'on se moquera de toi, toi que l'on appelle impure et féconde en iniquités.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Voilà que les princes de la maison d'Israël, chacun avec sa famille, ont conspiré en toi, afin de verser le sang.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 C'est chez toi qu'ils ont médit de leur père et de leur mère, qu'ils ont été iniques envers l'étranger, et qu'ils ont opprimé l'orphelin et la veuve.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Et ils ont méprisé mes choses saintes, et ils ont profané mes sabbats.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 Chez toi il est des voleurs prompts à verser le sang; chez toi ils ont mangé sur les hauts lieux, et ils ont commis des crimes au milieu de toi.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 Chez toi ils ont dévoilé la honte de leur père, et ils ont humilié la femme assise en sa souillure.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 Chez toi chacun a abusé de la femme de son prochain; chacun a souillé criminellement sa bru; chacun a humilié sa sœur et la fille de son père.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 Chez toi ils ont reçu des dons pour verser le sang; chez toi ils ont prêté à usure, et ont reçu plus qu'il ne leur était dû. Et tu as porté la méchanceté au comble par tes actes d'oppression; et moi, tu m'as oublié, dit le Seigneur.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Et si je frappe des mains au sujet des iniquités que tu as consommées, et de ton sang qui a été répandu au milieu de toi,
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Ton cœur se soutiendra-t-il? et tes mains conserveront-elles leur force en ces jours que je vais amener sur toi? C'est moi, dit le Seigneur, qui ai parlé, et j'exécuterai.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 Et je te disperserai parmi les gentils, et je te disséminerai en tous les royaumes, et ton impureté te sera ôtée.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 Et je ferai de toi mon héritage, aux yeux de toutes les nations; et vous saurez que je suis le Seigneur.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Fils de l'homme, voilà que la maison d'Israël est devenue pour moi comme un alliage d'airain, de fer, d'étain et de plomb, mêlé avec de l'argent.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 À cause de cela, dis-lui: Ainsi parle le Seigneur Maître: Parce que vous ne formez plus qu'un seul alliage, je vous recueillerai au milieu de Jérusalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 De même que dans la fournaise on rassemble l'argent, l'airain, le fer, l'étain et le plomb, pour souffler sur eux le feu et les fondre; ainsi je vous recueillerai en ma colère, et je vous rassemblerai, et je vous ferai fondre.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Et je soufflerai sur vous le feu de ma colère, et vous serez fondus au milieu de Jérusalem.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 De même que l'argent est fondu au milieu d'une fournaise, ainsi vous serez fondus au milieu de Jérusalem, et vous saurez que c'est moi, le Seigneur, qui ai versé sur vous ma colère.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 Fils de l'homme, dis à cette ville: Tu es une terre sans rosée; il n'est point venu de pluie sur toi au jour de ma colère.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 Ses princes au milieu d'elle sont comme des lions rugissants, ravissant leur proie, dévorant des âmes en leur violence, et recevant des présents. Et ils ont multiplié tes veuves au milieu de toi.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Et ses prêtres ont méprisé ma loi, et ils ont profané mes choses saintes. Ils n'ont point distingué le sacré du profane; ils n'ont point distingué le pur de l'impur; ils ont voilé leurs yeux pour ne point voir mes sabbats, et j'ai été déshonoré au milieu d'eux.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Ses princes au milieu d'elle sont comme des loups ravissant leur proie, prêts à verser le sang pour s'emparer du bien d'autrui.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Et ses prophètes qui caressent le peuple tomberont; ils ont des visions vaines, et ils annonceront des oracles menteurs, disant: Ainsi parle le Seigneur; quand le Seigneur n'a point parlé.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 Oppresseurs iniques du peuple de la terre, ravisseurs du bien d'autrui, spoliateurs du pauvre et de l'indigent, violateurs de la justice envers l'étranger!
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 J'ai cherché parmi eux un homme qui revînt à la droiture, qui se tînt devant ma face de toute son âme au temps de ma colère, pour ne point effacer entièrement cette ville, et je ne l'ai pas trouvé.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Et j'ai versé sur elle le feu de ma colère, pour la détruire, et j'ai fait retomber leurs voies sur leurs tètes, dit le Seigneur Maître.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”