< Ézéchiel 17 >

1 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, fais un récit, et dis ma parabole à la maison d'Israël.
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 Dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Un grand aigle, aux grandes ailes, à la vaste envergure, aux fortes serres, ayant dirigé son essor vers le Liban, y vint et choisit les meilleures branches d'un cèdre.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 Il arracha les pointes des bourgeons et il les transporta en la terre de Chanaan, et il les déposa dans une ville fortifiée.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 Et il prit de la graine en terre, et il la sema dans un champ fertilisé par beaucoup d'eau, et il la déposa en un lieu apparent.
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 Et elle germa, et elle devint une vigne basse et rampante, de sorte que les bourgeons apparaissaient au-dessus de la semence, tandis que les racines étaient en terre. Et elle devint une vigne, et elle provigna, et elle étendit en haut ses sarments.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 Et il vint un autre grand aigle, aux grandes ailes, aux serres nombreuses; et voilà que la vigne se plia autour de lui, et ses racines étaient près de lui, et elle lui envoya ses rameaux pour lui donner à boire de la sève de son plant.
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 Elle-même engraissa dans une bonne terre, sur des eaux abondantes, au point de pousser des jets, de porter des fruits, et d'être une grande vigne.
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Et à cause de cela, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Prospèrera-t-elle? Ses tendres racines, son fruit ne pourriront-ils pas? Ses bourgeons ne se dessècheront-ils pas? Ne sera-t-elle pas déracinée par un bras puissant et par un peuple nombreux?
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 Et voilà qu'elle a engraissé; mais pourra-t-elle s'élever? Ne sera-t- elle pas flétrie aussitôt que le vent brûlant la touchera? Oui, elle sera flétrie, avec la sève de ses bourgeons.
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 Fils de l'homme, dis à la maison qui m'irrite: Ne savez-vous pas ce que cela signifie? Dis encore: Quand le roi de Babylone viendra contre Jérusalem, il prendra son roi et ses princes, et il les emmènera avec lui à Babylone.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 Et il choisira un homme de famille royale, et il fera alliance avec lui, et il le liera par des serments; et il emmènera les princes de la terre,
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 Pour que le royaume soit affaibli, que le roi ne puisse se relever, qu'il garde son alliance et la maintienne.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 Mais si le roi se révolte contre lui, s'il envoie des émissaires en Égypte pour en obtenir des chevaux et une nombreuse armée, réussira-t-il, sera- t-il sauvé en agissant comme un ennemi? Sera-t-il sauvé en violant l'alliance?
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 Par ma vie, dit le Seigneur; il sera emmené où réside le roi qui l'a mis sur le trône, parce qu'il a méprisé le serment prêté en mon nom, et violé l'alliance où j'ai été pris à témoin, et il mourra au milieu de Babylone.
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 Et le Pharaon ne fera pas la guerre aux Assyriens avec une grande multitude et une forte armée, ni avec des retranchements et des balistes pour exterminer les âmes.
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 Et le roi de Jérusalem a méprisé son serment, et il a violé l'alliance, quand j'avais engagé sa main, et il a fait toutes ces choses pour sa sûreté, mais il ne sera pas sauvé.
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 À cause de cela, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Par ma vie, il a méprisé un serment prêté en mon nom, il a violé l'alliance où j'ai été pris à témoin, et je ferai retomber son crime sur sa tête.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 Et je jetterai sur lui un filet, et il sera pris au piège.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 Dans toutes les batailles, ses hommes périront par le glaive, et je disperserai leurs restes à tous les vents, et vous saurez que c'est moi, le Seigneur, qui ai parlé.
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 Car voici ce que dit le Seigneur: C'est moi qui prendrai sur la cime d'un cèdre ses plus belles branches; j'en retirerai la moelle, et je la planterai sur une haute montagne.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 Je la suspendrai sur la haute montagne d'Israël, et je la planterai; elle produira un rejeton, elle portera son fruit et deviendra un grand cèdre. Et chaque oiseau s'arrêtera sous ses branches, et tout ce qui vole se reposera sous son ombre, et ses rameaux seront pleins de force.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 Et tous les arbres des champs sauront que je suis le Seigneur, qui abaisse les grands arbres et élève les petits; qui dessèche l'arbre vert et fait reverdir l'arbre desséché. C'est moi, le Seigneur, qui ai parlé, et j'exécuterai.
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”

< Ézéchiel 17 >