< Ézéchiel 16 >

1 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, fais connaître à Jérusalem ses iniquités;
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 Et dis: Ainsi parle le Seigneur à Jérusalem: Ta racine et ton origine sortent de la terre de Chanaan; ton père était Amorrhéen, et ta mère une fille des Héthéens.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 Quant à ta naissance, le jour où tu as été enfantée, tu n'as point lié tes mamelles; tu n'as point été lavée dans l'eau; tu n'as point été salée avec du sel; tu n'as pas été enveloppée de langes.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Et mon œil ne s'est point apitoyé sur toi, et je ne t'ai fait aucune de ces choses, et je n'ai rien senti en ta faveur. Et tu as été jetée sur la terre d'un champ, dans la dépravation de ton âme, le jour où tu as été enfantée.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 Et j'ai passé près de toi, et je t'ai vue souillée de ton sang, et je t'ai dit: Que ta vie vienne de ton sang;
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Multiplie-toi! Et je t'ai faite comme l'herbe qui pousse dans les champs; et tu as crû, et tu as grandi, et tu es entrée dans les villes des villes. Et tes mamelles se sont gonflées, et tu es devenue nubile, et tu étais nue et confuse.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 Et j'ai passé près de toi, et je t'ai vue, et voilà que c'était ton temps, le temps où l'on dénoue les ceintures des vierges. Et j'ai étendu sur toi mes ailes, et j'ai caché ta nudité, et je t'ai fait des promesses, et j'ai fait alliance avec toi, dit le Seigneur. Et tu as été à moi.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Et je t'ai lavée dans l'eau, et j'ai enlevé le sang qui te souillait, et je t'ai parfumée d'huile.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 Et je t'ai vêtue de robes brodées, et je t'ai chaussée d'hyacinthe, et je t'ai ceinte de fin lin, et je t'ai enveloppée des tissus les plus délicats.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Et je t'ai parée de joyaux; je t'ai mis des bracelets et un collier.
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 Et je t'ai donné un anneau pour tes narines, et je t'ai mis des boucles d'oreilles, et j'ai posé sur ta tête une couronne de gloire.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Et tu as été ornée d'or et d'argent, et tes voiles étaient de fin lin, et ils étaient délicatement tissus, et ils étaient brodés. Et tu te nourrissais de fleur de farine, de miel et d'huile, et tu es devenue merveilleusement belle.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Et ta renommée s'est répandue parmi les nations, à cause de ta beauté; car elle était accomplie par la convenance, par le charme que j'avais mis en toi, dit le Seigneur.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Mais tu t'es confiée en ta beauté, tu t'es prostituée au milieu de ta gloire; et tu t'es livrée à la fornication avec tous les passants.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Et tu as pris tes vêtements; et tu en as fabriqué des idoles; et tu t'es prostituée sur elles, et tu ne peux aller plus loin, et nul ne le pourra.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Et tu as pris tes parures de gloire, faites de mon argent et de mon or, et tu en as fabriqué pour toi des images d'hommes auxquelles tu t'es prostituée.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 Et tu as pris tes robes brodées, et tu les en as revêtues; et tu leur as fait offrande de mon huile et de mes parfums,
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Et de mes pains que je t'avais donnés (car je te nourrissais de fleur de farine, d'huile et de miel); et tu les as posés devant ces idoles en odeur de suavité. Et voici ce qui est advenu, dit le Seigneur.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Tu as pris tes fils et tes filles que tu avais engendrés, et tu les leur as sacrifiés, pour qu'ils soient consumés par le feu. Et comme si c'était peu de t'être ainsi prostituée,
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 Tu as égorgé tes enfants pour les livrer à tes idoles, comme des victimes expiatoires.
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 Mais ceci dépasse toute ton infamie: tu ne t'es point souvenue de ta jeunesse, quand tu étais nue et confuse, et que tu vivais souillée dans ton sang.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 Et voici ce qui est advenu après toutes tes abominations, dit le Seigneur:
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 Tu as bâti pour toi une maison de débauche, et tu t'es affichée toi-même sur toutes les places;
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 Et à chaque coin de rue tu as bâti tes lieux de prostitution; et tu as souillé ta beauté, tu as livré les membres à tous les passants, tu as multiplié tes débauches,
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Et tu t'es prostituée aux fils de l'Égypte, tes voisins, peuple charnu, et tu t'es prostituée de toute manière, au point de provoquer ma colère.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Mais je vais étendre la main contre toi; et je déracinerai tes habitudes, et je te livrerai aux âmes qui te haïssent, aux filles des étrangers, qui rougissent elles-mêmes de la voie où tu as commis tes impiétés.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Et tu t'es prostituée avec les filles d'Assur, et même ainsi tu n'as pas été assouvie; tu t'es prostituée, et tu n'as pas été rassasiée.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Et tu as multiplié tes alliances en la terre des Chaldéens, et tu n'as pas été rassasiée.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 Comment ferais-je alliance avec ta fille, dit le Seigneur, pendant que tu fais toutes les œuvres d'une femme prostituée? Or tu as triplé, tes débauches en tes filles.
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 Tu as bâti une maison de débauche à chaque coin de rue; tu as des lieux de prostitution sur toutes les places. Et tu es devenue comme une prostituée, qui met toujours ses faveurs à plus haut prix.
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 Une femme adultère te ressemble; elle prend l'argent que gagne son mari,
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 Et le donne à tous ceux à qui elle s'est prostituée. De même tu as donné tes salaires à tous tes amants, et tu les as chargés de présents, pour qu'ils vinssent à toi de toutes parts en ta prostitution.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 Car tu as agi autrement que les autres femmes en ta prostitution, envers ceux à qui tu t'es prostituée: c'est toi qui les as payés, et aucun salaire ne t'a été donné; et voilà comment a tourné ta perversité.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 À cause de cela, prostituée, écoute la parole du Seigneur.
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que tu as prodigué ton argent monnayé, ta honte sera dévoilée dans ta prostitution à tes amants, dans toutes tes pensées, dans tes abominations et dans le sang de tes enfants, que tu as livrés à tes idoles.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 À cause de cela, voilà que je vais rassembler contre toi tous les amants à qui tu t'es donnée; et tous ceux que tu as aimés, je les réunirai à ceux que tu haïssais. Et je les placerai en cercle autour de toi, et je leur dévoilerai tes iniquités, et ils verront toute ta honte.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Et je te punirai comme on punit la femme adultère, et je te plongerai dans le sang de la fureur et de la jalousie.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Et je te livrerai à leurs mains, et ils démoliront ta maison de débauche, et ils détruiront les lieux où tu te prostituais, et ils te dépouilleront de tes vêtements, et ils te prendront ta parure de gloire, et ils te chasseront nue et confuse;
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Et ils te feront poursuivre par la populace, et ils te lapideront, et ils t'égorgeront avec leurs glaives.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 Et ils brûleront ta maison par le feu, et ils tireront vengeance de toi devant un grand nombre de femmes. Et je te détournerai de la débauche, et je ne te permettrai plus de donner des salaires.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Alors je ne déchaînerai plus ma fureur contre toi, et ma jalousie se détournera de toi, et je me tiendrai en repos, et je n'aurai plus souci de toi.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 En punition de ce que tu ne t'es point souvenue de ta jeunesse, et que tu m'as contristé par toutes ces choses, voilà que j'ai rétribué toutes tes voies sur ta tête, dit le Seigneur; car tu as mis le comble à tes désordres par ton impiété.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Toutes ces choses font que l'on dit de toi en proverbe: Telle fut la mère,
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Telle est la fille de la mère; tu es celle qui as répudié son époux et ses enfants, et les sœurs de tes sœurs ont répudié leurs époux et leurs enfants. Ta mère était Héthéenne, et ton père Amorrhéen.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Samarie est votre sœur aînée; elle et sa fille habitent à ta gauche. Et ta plus jeune sœur, qui habite à ta droite, c'est Sodome et ses filles.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Et tu n'as pas seulement marché comme elles en leurs voies, tu ne t'es pas contentée de leurs abominations; mais encore en tes voies tu les as surpassées.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Par ma vie, dit le Seigneur, Sodome et ses filles n'ont pas fait comme vous avez fait, toi et tes filles.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Or voici l'iniquité de Sodome, ta sœur; c'est l'orgueil; elle et ses filles nageaient dans la prospérité, dans l'abondance du pain, dans l'excès des plaisirs; elles avaient tout cela, et jamais elles n'ont tendu la main au pauvre ni au mendiant.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 Elles se sont donc enorgueillies, et elles ont fait des iniquités devant moi, et je les ai détruites comme je l'ai jugé bon.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Samarie, de son côté, n'a point péché moitié autant que toi; mais tu les as surpassées l'une et l'autre en abominations; et tu as tellement multiplié tes iniquités, que tes sœurs en ont paru justes.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Reçois donc ton châtiment, parce que tu as corrompu tes sœurs par tes péchés que tu as multipliés plus qu'elles; ce qui les a fait paraître plus justes que toi. Rougis donc, et accepte ton ignominie, car tu as justifié tes sœurs.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 Et je ferai revenir leurs captifs; je relèverai Sodome et ses filles, je relèverai Samarie et ses filles, et je te relèverai toi-même au milieu d'elles,
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 Afin que tu acceptes ton châtiment et que tu sois confuse de tout ce que tu as fait pour m'irriter.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Et ta sœur Sodome et ses filles seront rétablies comme elles étaient au commencement; et toi-même et tes filles, vous serez rétablies comme vous étiez au commencement.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Certes, on n'a pas entendu le nom de Sodome, ta sœur, sortir de ta bouche aux jours de ta superbe,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 Avant que tes méchancetés eussent été dévoilées. De même, tu es aujourd'hui un sujet d'opprobre pour les filles de la Syrie et pour les filles de tous ceux qui l'entourent, et pour toutes les filles des Philistins qui forment un cercle autour de toi.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Quant à tes impiétés et à tes crimes, tu en as porté peine, dit le Seigneur.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 Or voici ce que dit le Seigneur: Comme tu as agi, j'agirai envers toi, puisque tu méprises tes promesses en violant mon alliance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Mais je me souviendrai de l'alliance que j'ai faite avec toi dans ta jeunesse, et je la ferai revivre, et ce sera une alliance éternelle.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Et tu te souviendras de ta voie, et tu seras couverte de honte, lorsque tu recevras tes sœurs aînées et tes sœurs puînées, et je te les donnerai pour que tu les réédifies, mais non par une alliance qui vienne de toi.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 Et je ferai revivre mon alliance avec toi, et tu connaîtras que je suis le Seigneur;
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 Afin que tu te souviennes, et que tu rougisses, sans oser même ouvrir la bouche en face de ta honte, lorsque je t'aurai pardonné tout ce que tu as fait, dit le Seigneur.
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ézéchiel 16 >