< Ézéchiel 12 >
1 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
2 Fils de l'homme, tu demeures au milieu des iniquités de ceux qui ont des yeux pour voir, et ne voient point; qui ont des oreilles pour entendre, et n'entendent point; car c'est une maison qui m'irrite.
ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
3 Et maintenant, fils de l'homme, prépare ton bagage, pour aller en captivité devant eux en plein jour; et devant eux tu seras emmené captif de ce lieu en un autre lieu, afin qu'ils te voient; car c'est une maison qui m'irrite.
“Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
4 Et tu transporteras ton bagage pour aller en captivité devant eux, en plein jour; puis, sous leurs yeux, tu sortiras le soir, comme sort un captif.
Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
5 Creuse-toi un trou dans le mur de ta maison, et tu passeras par ce trou,
Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
6 Devant eux. Tu te feras porter sur des épaules, et tu sortiras dans les ténèbres; tu te cacheras le visage, et tu ne verras pas la terre; car je t'ai donné comme un signe à la maison d'Israël.
Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
7 Et je fis toutes ces choses, comme le Seigneur me l'avait commandé, et je transportai en plein jour mon bagage pour aller en captivité; et le soir je fis pour moi un trou au mur, et je sortis dans les ténèbres, et je me fis porter sur des épaules devant eux.
Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
8 Et le matin, la parole du Seigneur me vint, disant:
Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Fils de l'homme, la maison d'Israël, cette maison qui m'irrite, n'a-t-elle pas dit: Que fais-tu?
“Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
10 Dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Moi, le prince et le chef de Jérusalem, à tout le peuple d'Israël, à tous ceux qui sont dans la ville,
“Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
11 J'ai dit: Je fais pour eux des signes; et comme j'ai fait, il leur adviendra. Ils partiront pour l'exil et la captivité.
Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
12 Et, au milieu d'eux, le roi sera porté sur des épaules, et il sortira dans les ténèbres, par une brèche de mur, et il aura fait cette brèche pour sortir; il se cachera le visage, de sorte que nul œil ne le verra, et lui-même ne verra pas la terre.
“Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
13 Et je tendrai mon filet sur lui, et il y sera pris, et je le conduirai à Babylone, en la terre des Chaldéens; et il ne la verra pas, et il y mourra.
Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
14 Et tous ses auxiliaires d'alentour, et tous ses alliés, je les disperserai à tous les vents, et je les poursuivrai à coups d'épée.
Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
15 Et ils connaîtront que je suis le Seigneur, quand je les aurai dispersés parmi les nations, et ils seront dispersés dans toutes les contrées.
“Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
16 Et parmi eux je ferai échapper un petit nombre d'hommes au glaive, à la famine et à la peste, afin qu'ils racontent toutes leurs iniquités chez les nations où ils iront résider, et qu'elles sachent que je suis le Seigneur.
Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
17 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Fils de l'homme, mange ton pain dans la tristesse; bois ton eau dans les tourments et l'affliction.
“Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
19 Et dis au peuple de la terre: Ainsi parle le Seigneur à ceux qui demeurent à Jérusalem et sur le territoire d'Israël: Ils mangeront le pain dans la détresse, et ils boiront leur eau dans la désolation, lorsque cette terre sera détruite avec sa richesse; car tous ceux qui l'habitent vivent dans l'impiété.
Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
20 Et je rendrai désertes leurs villes si peuplées, et leur terre sera dévastée; et vous saurez que je suis le Seigneur.
Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
21 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
22 Fils de l'homme, quelle est cette parabole que l'on dit sur la terre: Les jours sont loin, la vision a péri?
“Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
23 À cause de cela, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Je changerai cette parabole, et on ne répètera plus cette parabole en la maison d'Israël; car tu lui diras: Les jours sont proches, et toutes les paroles de la vision.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
24 Car il n'y aura plus de vision fausse, ni de faux prophètes qui prédisent au milieu des fils d'Israël pour leur plaire.
Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
25 Car moi-même, le Seigneur, je dirai mes paroles; je parlerai et j'exécuterai, et je ne différerai plus; car c'est en ces jours mêmes où cette maison m'irrite, que je vais parler, et j'exécuterai, dit le Seigneur.
Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
26 Et la parole du Seigneur me vint, disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
27 Fils de l'homme, voilà que la maison d'Israël m'irrite; ils disent: La vision que cet homme a eue est pour des jours lointains, et il prophétise ainsi pour des temps loin de nous.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
28 À cause de cela, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: La parole que j'ai dite ne tardera pas à s'accomplir: je vais parler et j'exécuterai, dit le Seigneur.
“Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”