< Ézéchiel 1 >

1 Et il arriva que, en ma trentième année, le quatrième mois, le cinquième jour du mois, j'étais assis au milieu des captifs, sur le fleuve Chobar; et les cieux furent ouverts, et j'eus les visions de Dieu.
A shekara ta talatin, a wata na huɗu a rana biyar, yayinda nake cikin’yan zaman bauta kusa da Kogin Kebar, sai sammai suka buɗe na kuwa ga wahayoyin Allah.
2 Le cinquième jour de ce mois, en cette année, la cinquième de la captivité du roi Joakim,
A rana biyar ga wata, a shekara ta biyar ne ta zaman bautan Sarki Yehohiyacin,
3 La parole du Seigneur vint à Ezéchiel, fils de Buzi, le prêtre, en la terre des Chaldéens, sur le fleuve Chobar. Et la main du Seigneur fut sur moi.
maganar Ubangiji ta zo wa Ezekiyel firist, ɗan Buzi, kusa da Kogin Kebar a ƙasar Babiloniyawa. A can hannun Ubangiji yana a kansa.
4 Et je vis, et voilà qu'un vent violent vint de l'aquilon, et avec lui une grande nuée, et tout alentour une lueur et un feu brillant, et, au milieu, comme une vision d'émail au milieu du feu, et cet émail était lumineux.
Na duba, sai na ga guguwa ta taso daga arewa babban hadari cike da walƙiya kewaye da haske mai haske sosai. Tsakiyar wutar ta yi kamar ƙarfe mai cin wuta balbal,
5 Et au milieu du feu il y avait comme la ressemblance de quatre animaux, et voici leur aspect: il y avait en eux la ressemblance d'un homme;
a cikin wutar kuwa akwai abin da ya yi kamar halittu guda huɗu. A bayyane kamanninsu ya yi kamar siffar mutum,
6 Et à chacun quatre faces, et à chacun quatre ailes,
amma kowannensu yana da fuskoki huɗu da fikafikai guda huɗu.
7 Et leurs jambes étaient droites, et leurs pieds ailés; et ils lançaient des étincelles, comme de l'airain brillant. Et leurs ailes étaient légères,
Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne; kuma ƙafafunsu sun yi kamar na maraƙi suna kuma walƙiya kamar tagullar da aka goge.
8 Et il y avait une main d'homme sous leurs ailes, aux quatre côtés.
A ƙarƙashin fikafikansu huɗu suna da hannuwan mutum a kowane gefe. Dukansu huɗu suna da fuskoki da fikafikai,
9 Et les faces de ces quatre animaux ne se retournaient pas, quand ils marchaient; ils allaient chacun droit devant sa face.
kuma fikafikansu suna taɓan juna. Kowanne ya miƙe gaba; ba sa juyawa sa’ad da suke tafiya.
10 Et voici la ressemblance de leurs faces: une face d'homme et une face de lion à droite des quatre, une face de veau à gauche des quatre, et une face d'aigle aux quatre.
Fuskokinsu sun yi kamar haka. Kowanne a cikin huɗun yana da fuskar mutum, kuma a gefen dama kowanne yana da fuskar zaki, a hagu kuma fuskar maraƙi; kowanne yana kuma da fuskar gaggafa.
11 Et quatre ailes étaient étendues au-dessus d'eux; deux de ces ailes les joignaient l'un à l'autre, et deux couvraient leur corps.
Haka fuskokinsu suka kasance. Fikafikansu sun buɗu sama; kowanne yana da fikafikai biyu, ɗaya yana taɓa fikafikan ɗayan halittar a ɗayan gefe, fikafikai biyu kuma suna rufe jikinsa.
12 Et chacun marchait droit en avant; où le vent allait, ils allaient, et ils ne se retournaient pas.
Kowanne ya miƙe gaba sosai. Duk inda ruhu zai tafi, can za su, ba tare da juyawa ba yayinda suke tafiya.
13 Et au milieu des animaux, il y avait comme une vision de charbons en feu, comme une vision de lampes courant ensemble entre les animaux, et une flamme éclatante, et de la flamme sortaient des éclairs.
Kamannin halittun ya yi kamar garwashi mai cin wuta ko kuwa kamar fitilu. Wuta tana kai da kawowa a cikin halittun; ta yi haske ƙwarai, walƙiya kuma tana wulgawa daga cikinta.
14 Et je vis, et voilà qu'il y avait une roue sur la terre auprès des quatre animaux,
Halittun suna gaggauta kai da kawowa kamar walƙiya.
15 Et je vis, et voilà qu'il y avait une roue sur la terre auprès des quatre animaux,
Yayinda nake kallon rayayyun halittun nan, sai na ga da’ira a ƙasa kusa da kowace halitta da fuskokinsa huɗu.
16 Et l'aspect des roues était comme l'aspect de Tharsis, et toutes les quatre étaient semblables. Et elles étaient faites comme s'il y avait eu une roue dans une roue.
Ga kamanni da fasalin da’irorin. Suna ƙyalƙyali kamar kirisolit, kuma dukan huɗun sun yi kama da juna. Kowacce ta yi kamar da’ira a cikin da’ira.
17 Et elles allaient sur leurs quatre parties, et elles ne se retournaient pas en marchant,
Yayinda suke tafiya, sukan nufi duk wani gefe guda cikin gefe huɗun da halittun suka nufa; da’irorin ba za su juya ba sa’ad da halittun suke tafiya.
18 Ni elles ni leurs moyeux; et elles étaient hautes; et je vis leurs parties, et leurs moyeux étaient remplis d'yeux, aux quatre circonférences.
Ƙarafansu da suka yi kamar zobe sun yi tsayi suna kuma da bantsoro, dukan ƙarafan nan huɗu kuwa da suka yi kamar zobe suna cike da idanu a kewaye.
19 Et quand les animaux marchaient, les quatre roues à côté d'eux marchaient, et quand les animaux s'élevaient au-dessus de terre, les roues s'élevaient.
Sa’ad da rayayyun halittun suke tafiya, da’irorin da suke kusa da su kan motsa; kuma sa’ad da rayayyun halittun sun tashi sama, da’irorin su ma sukan tashi sama.
20 Et partout où était la nuée, là aussi le vent soufflait; et les roues marchaient et s'élevaient avec les animaux; car un souffle de vie était dans les roues.
Duk inda ruhu za shi, su ma can za su, kuma da’irorin za su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
21 Quand les animaux marchaient, elles marchaient; quand ils s'arrêtaient, elles s'arrêtaient, et quand ils s'élevaient au-dessus de la terre, elles s'élevaient avec eux; car un souffle de vie était dans les roues.
Sa’ad da halittun sun motsa, sai su ma su motsa; sa’ad da halittun sun tsaya cik, su ma sai su tsaya cik, sa’ad da kuma halittun sukan tashi sama, da’irorin suka tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
22 Et au-dessus de la tête des animaux il y avait une image comme celle d'un firmament, semblable à du cristal, qui s'étendait au-dessus de leurs ailes.
A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.
23 Et, au-dessus du firmament, leurs ailes étaient étendues, battant l'une contre l'autre, et celles de dessous couvrant leurs corps.
A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.
24 Et j'entendis le bruit de leurs ailes pendant qu'ils marchaient, comme la voix des grandes eaux; et quand ils s'arrêtaient, leurs ailes se reposaient.
Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.
25 Et voilà qu'une voix sortit du firmament qui était au-dessus de leurs tètes,
Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.
26 Et qui ressemblait à un saphir, et qui supportait l'image d'un trône, sur lequel était une image semblable à un homme.
A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.
27 Et je vis comme une vision d'émail, depuis ses reins jusqu'en haut; et depuis ses reins jusqu'en bas je vis une vision de feu, et sa lueur formait un cercle,
Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.
28 Semblable à l'arc qui est dans la nuée les jours de pluie; telle était la forme de cette lueur en cercle. C'est ainsi que je vis l'image de la gloire du Seigneur; je la vis, et je tombai la face contre terre, et j'entendis la voix d'un esprit qui parlait.
Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.

< Ézéchiel 1 >