< Exode 2 >

1 Or, il y avait un homme de la tribu de Lévi qui épousa une des filles de Lévi.
Ana nan, sai wani Balawe ya auri wata Balawiya,
2 Elle conçut, et elle enfanta un garçon, et, l'ayant vu plein de grâces, ils le cachèrent pendant trois lunes.
ta kuwa yi ciki, ta haifi ɗa. Sa’ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har watanni uku.
3 Lorsqu'ils ne purent le cacher plus longtemps, sa mère prépara pour lui une corbeille qu'elle couvrit d'un enduit de poix et de bitume; elle y plaça l'enfant, et elle posa la corbeille dans le marais sur la rive du fleuve.
Amma da ba tă iya ɓoye shi kuma ba, sai ta yi kwandon kyauro ta shafa masa kwalta. Bayan haka sai ta sa jaririn a cikin kwandon, ta je ta ajiye kwandon tare da jaririn a cikin kyauro, a bakin kogin.
4 Comme la sœur de l'enfant observait de loin pour savoir ce qu'il deviendrait.
’Yar’uwarsa ta tsaya da ɗan rata tana lura da abin da zai faru da shi.
5 La fille du Pharaon descendit au fleuve pour se baigner, tandis que ses servantes se promenaient sur la rive; elle aperçut dans le marais la corbeille, et elle envoya une servante, qui la retira.
Sai’yar Fir’auna ta gangara zuwa kogi domin tă yi wanka, bayinta kuwa suna tafiya a bakin kogi. Sai ta ga kwandon a ciyawa, ta aiki ɗaya daga cikin masu hidimarta tă ɗauko mata.
6 L'ayant ouverte, elle vit un enfant pleurant dans la corbeille; aussitôt la fille du Pharaon résolut de le sauver, et elle dit: C'est un enfant des Hébreux.
Da ta buɗe kwandon, sai ta ga yaro yana kuka, ta kuwa ji tausayinsa. Ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin jariran Ibraniyawa ne.”
7 Et la sœur dit à la fille du Pharaon: Veux-tu que je t'appelle une nourrice, parmi les femmes des hébreux, pour allaiter l'enfant?
Sai’yar’uwarsa ta tambayi’yar Fir’auna, ta ce, “In tafi in samo ɗaya daga cikin matan Ibraniyawa tă yi miki renon yaron?”
8 Va, dit la fille du Pharaon; et la jeune fille, étant partie, appela la mère de l'enfant.
Sai ta amsa ta ce, “I, tafi.” Sai yarinyar ta tafi ta kawo mahaifiyar yaron.
9 La fille du Pharaon dit à celle-ci: Soigne-moi cet enfant, et allaite-le, je te donnerai une récompense; la femme prit donc l'enfant et l'allaita.
Diyar Fir’auna ta ce mata, “Ɗauki jaririn, ki yi mini renonsa, zan kuwa biya ki.” Saboda haka ta ɗauki yaron, ta yi renonsa.
10 L'enfant s'étant développé, elle le conduisit à la fille du Pharaon; et il fut pour elle comme un fils, et elle le nomma Moïse, car, dit-elle, nous l'avons retiré de l'eau.
Sa’ad da ya yi girma, sai ta kawo shi wajen’yar Fir’auna, ya kuwa zama ɗanta, ta kuma ba shi suna Musa, tana cewa, “Na tsamo shi daga ruwa.”
11 Or, il arriva qu'après bien des jours, Moïse, étant devenu un homme, sortit près de ses frères les fils d'Israël; il pensait à leurs souffrances, lorsqu'il aperçut un Égyptien qui frappait un Hébreu, l'un de ses frères les enfants d'Israël.
Wata rana, bayan Musa ya yi girma, sai ya haura, ya tafi inda mutanensa suke, ya kuma ga yadda suke shan wahala da aiki. Ya ga wani mutumin Masar yana dūkan mutumin Ibraniyawa, ɗaya daga cikin mutanensa.
12 Après avoir regardé tout alentour, ne voyant personne, il tua l'Égyptien, et il l'enfouit dans le sable.
Da ya leƙa nan da can bai kuwa ga kowa ba, sai ya kashe mutumin Masar, ya ɓoye shi a yashi.
13 Le jour suivant, étant sorti, il vit deux Hébreux en venir aux mains, e il dit à celui qui avait tort: Pourquoi frappes-tu ton frère?
Kashegari ya fita, sai ya ga Ibraniyawa biyu suna faɗa. Ya tambayi mai laifin ya ce, “Don me kake bugun ɗan’uwanka, mutumin Ibraniyawa?”
14 Celui-ci dit: Qui t'a établi chef et juge sur nous? Veux-tu me tuer comme tu as tué hier l'Égyptien? Moïse fut saisi de crainte, et il se dit: La chose est-elle connue à ce point?
Mutumin ya ce masa, “Wa ya mai da kai mai mulki da mai hukunci a kanmu? Kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan?” Sai Musa ya tsorata, ya yi tunani ya ce, “To, fa, abin nan da na yi, ya zama sananne.”
15 Le Pharaon, l'ayant apprise, voulut faire périr Moïse; mais celui-ci s'éloigna de la face du Pharaon; il passa en la terre de Madian, et, étant arrivé en la terre de Madian, il s'assit auprès d'un puits.
Da Fir’auna ya ji wannan, sai ya yi ƙoƙari yă kashe Musa, amma Musa ya gudu daga wajen Fir’auna, ya tafi ƙasar Midiyan inda ya zauna kusa da wata rijiya.
16 Or, le prêtre de Madian avait sept filles qui paissaient les brebis de leur père Jéthro; et elles vinrent puiser de l'eau jusqu'à ce qu'elles eussent rempli les abreuvoirs, et fait boire les brebis de leur père Jéthro.
To, fa, akwai wani firist na Midiyan, yana da’ya’ya mata bakwai, suka zo su shayar da dabbobin mahaifinsu.
17 Des pâtres, étant survenus, les chassèrent; mais Moïse, s'étant levé, les délivra; il puisa de l'eau pour elles, et abreuva leurs brebis.
Sai waɗansu makiyaya suka zo suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su ya shayar da dabbobinsu.
18 Lorsqu'elles furent de retour chez Raguel, leur père, il leur dit: Pourquoi revenez-vous sitôt aujourd'hui?
Da’yan matan suka komo wurin Reyuwel mahaifinsu, sai ya tambaye su ya ce, “Yaya kuka dawo da wuri yau?”
19 Elles lui répondirent: Un Égyptien nous a défendues contre les pâtres; il a puisé de l'eau pour nous, et a fait boire nos brebis.
Suka amsa suka ce, “Wani mutumin Masar ne ya taimake mu daga hannun waɗansu makiyaya. Har ma ya ɗebo ruwa ya shayar da dabbobin.”
20 Et il dit à ses filles: Où est-il? Pourquoi avez-vous laissé là cet homme? Appelez-le donc, et qu'il mange de notre pain.
Ya tambayi’yan matansa, “To ina yake? Don me kuka bar shi a can? A gayyace shi, yă zo, yă ci wani abu.”
21 Et Moïse demeura chez l'homme, qui bientôt donna pour femme à Moïse sa fille Séphora.
Musa ya yarda yă zauna da mutumin wanda ya ba da’yarsa Ziffora aure da Musa.
22 Celle-ci conçut, et elle enfanta un fils, que Moïse nomma Gersam: Car, dit-il, je suis passager en une terre étrangère.
Ziffora ta haifi wa Musa ɗa, ya kuma raɗa masa suna Gershom cewa, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa.”
23 Cependant, après un grand nombre de jours mourut le roi d'Égypte; en ce temps-là les fils d'Israël gémissaient à cause de leurs travaux, et poussaient des cris de douleur, et les cris qu'ils jetèrent, à cause de leurs travaux, montèrent jusqu'à Dieu.
Ana nan dai, a kwana a tashi, sai sarkin Masar ya mutu. Isra’ilawa suka yi kuka mai zafi saboda bautarsu mai wuya, sai kukar neman taimakonsu saboda bauta, ya kai wurin Allah.
24 Et il entendit leurs gémissements: il se souvint de son alliance avec Abraham, Isaac et Jacob.
Allah kuwa ya ji kukansu sai ya tuna da alkawarinsa da Ibrahim da Ishaku da Yaƙub.
25 Et Dieu regarda les fils d'Israël, et se fit connaître à eux.
Sai Allah ya dubi Isra’ilawa, ya kuma damu da su.

< Exode 2 >