< Exode 17 >
1 Après avoir quitté le désert de Sin, la synagogue des fils d'Israël établit ses campements comme le prescrivit le Seigneur et campa en Rhaphidin, où il n'y avait point d'eau à boire pour le peuple.
Dukan taron Isra’ilawa suka kama tafiya daga Hamadar Sin, suka yi ta tafiya suna sauka a wurare dabam-dabam bisa ga umarnin Ubangiji. A ƙarshe suka sauka a Refidim, suka zauna a can, amma ba ruwan da jama’a za su sha.
2 Alors, le peuple injuria Moïse, disant: Donne-nous de l'eau, afin que nous buvions; et Moïse leur dit: Pourquoi m'injuriez-vous? Pourquoi tentez- vous le Seigneur?
Saboda haka suka yi wa Musa maganganun banza suka ce, “Ba mu ruwa mu sha.” Musa ya amsa ya ce, “Don me kuke mini maganganun banza? Don me kuke gwada Ubangiji?”
3 En ce lieu, le peuple souffrit de la soif, et le peuple murmura contre Moïse, disant: Qu'as-tu fait? Nous as-tu tirés de l'Égypte pour nous faire mourir de soif, nous, et nos enfants et notre bétail?
Amma mutanen suka yi fama da ƙishirwa a can, suka yi gunaguni a kan Musa. Suka ce, “Don me ka fitar da mu daga Masar, ka sa mu da’ya’yanmu da dabbobinmu, mu mutu da ƙishirwa?”
4 Moïse aussitôt cria au Seigneur, disant: Que ferai-je à ce peuple! Encore un peu, et ils me lapideront.
Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Me zan yi da wannan jama’a? Suna shiri su jajjefe ni da duwatsu.”
5 Et le Seigneur dit à Moïse: Avance-toi en face de ce peuple, prends avec toi quelques-uns des anciens du peuple, prends à la main la baguette avec laquelle tu as frappé le fleuve, et pars.
Ubangiji amsa wa Musa, “Ka ɗauki sandan da ka bugi ruwan Nilu da shi. Ka kira waɗansu shugabannin Isra’ila, ku wuce a gaban jama’ar.
6 Et moi je me tiens, avant que tu y arrives, sur les rochers d'Horeb; là tu frapperas la pierre; il en sortira de l'eau, et le peuple boira. Ainsi fit Moïse devant les fils d'Israël.
Zan tsaya a can a gabanka, kusa da dutsen Horeb. Ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito daga gare shi domin mutane su sha.” Sai Musa ya yi haka a idon dattawan Isra’ila.
7 Et il nomma ce lieu: Tentation et Outrage, à cause des injures des fils d'Israël, et parce qu'ils avaient tenté le Seigneur, disant: Le Seigneur est- il avec nous, oui ou non?
Sai suka ba wa wurin suna, Massa da Meriba, saboda Isra’ilawa sun yi jayayya, suka kuma gwada Ubangiji cewa, “Ubangiji yana tsakaninmu ko babu?”
8 Peu après, Amalec vint apporter la guerre à Israël en Rhaphidin.
Amalekawa suka zo, suka yaƙi Isra’ilawa a Refidim.
9 Et Moïse dit à Josué: Choisis avec toi les hommes forts; sors à leur tête demain matin, et range-les en bataille devant Amalec; cependant, je me tiendrai sur la cime du mont, la baguette de Dieu à la main.
Musa ya ce wa Yoshuwa, “Zaɓi waɗansu mazanmu, ka je ka yaƙi Amalekawa. Gobe zan tsaya a bisa tudu, da sandan Allah a hannuwana.”
10 Josué fit ce que lui avait prescrit Moïse; il sortit, se rangea en bataille devant Amalec, et Moïse, avec Aaron et Hur, monta sur la cime du mont.
Sai Yoshuwa ya yaƙi Amalekawa kamar yadda Musa ya umarta, Musa, Haruna da Hur kuwa suka tafi bisa tudu.
11 Or, il advint que, lorsque Moïse levait les bras, Israël l'emportait; mais quand il les baissait, Amalec triomphait.
Muddin hannun Musa yana a miƙe, sai Isra’ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara.
12 Comme ses bras se fatiguaient, Hur et Aaron placèrent sous lui une pierre, sur laquelle il s'assit; puis, Aaron et Hur soutinrent ses bras l'un d'un côté, l'autre de l'autre; et les bras de Moïse furent soutenus jusqu'au coucher du soleil.
Sa’ad da hannuwan Musa suka gaji, sai Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka sa ya zauna a kai. Sa’an nan su kuma suka tsaya gefe da gefe, suna riƙe da hannuwansa har fāɗuwar rana.
13 Josué mit en fuite Amalec, et il passa tout son peuple au fil de l'épée.
Sai Yoshuwa kuwa ya ci nasara a kan Amalekawa da takobi.
14 Et le Seigneur dit à Moïse: Écris cela sur un livre, que ce soit un mémorial; ensuite dis à Josué cette parole: J'effacerai de la terre le souvenir d'Amalec.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka rubuta wannan a cikin littafi, yă zama abin tuni, ka kuma faɗa wa Yoshuwa zan hallaka Amalekawa ƙaƙaf daga duniya.”
15 Et Moïse bâtit au Seigneur un autel, qu'il nomma: le Seigneur est mon refuge.
Musa ya gina bagade, sai ya kira shi Ubangiji shi ne Tutata.
16 Car, dit-il, le Seigneur, d'une main inflexible, combattra contre Amalec de génération en génération.
Ya ce, “Gama an ɗaga hannuwa sama zuwa kursiyin Ubangiji, Ubangiji zai yaƙi Amalekawa daga tsara zuwa tsara.”