< Deutéronome 13 >
1 S'il s'élève parmi vous un prophète ou un songeur ayant des songes, s'il vous annonce un signe ou un prodige,
In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
2 Si le signe ou le prodige dont il aura parlé se fait, et s'il dit: Allons, servons d'autres dieux qui vous sont inconnus,
in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
3 Vous n'écouterez point ce prophète ou ce songeur; car le Seigneur votre Dieu vous tente, pour savoir si vous l'aimez de tout votre cœur et de toute votre âme.
kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
4 Vous suivrez le Seigneur votre Dieu; vous le craindrez; vous serez dociles à sa parole; vous vous attacherez à lui;
Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
5 Et ce prophète ou songeur mourra, parce qu'il aura parlé pour t'égarer loin du Seigneur ton Dieu qui t'a fait sortir de la terre d'Egypte, qui t'a délivré de la servitude; il aura parlé pour t'entraîner hors de la voie où le Seigneur ton Dieu t'a prescrit de marcher; vous détruirez parmi vous le mal.
Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
6 Et, si ton frère de père ou de mère, si ton fils, ta fille, ta femme qui repose sur ton sein, si l'ami que tu aimes comme ta vie, t'exhortent en secret, disant: Allons, servons d'autres dieux inconnus de tes pères et de toi,
In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
7 Des dieux des nations qui vous entourent de près ou de loin, d'une extrémité à l'autre de la terre,
allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
8 Tu n'y consentiras point, tu ne l'écouteras point; ton œil ne prendra pas en pitié sa faute; tu ne soupireras pas pour lui, tu ne le cacheras point;
kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
9 Tu le feras connaître, tu le signaleras; tes mains s'élèveront les premières contre lui pour qu'il périsse; les mains du peuple viendront après.
Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
10 Il sera lapidé, il mourra pour avoir cherché à te détourner du Seigneur ton Dieu qui t'a fait sortir de l'Egypte et de la maison de servitude.
Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
11 Tout Israël en l'apprenant aura crainte, et l'on évitera parmi vous de faire de nouveau un tel mal.
Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
12 Et si, en l'une des villes que le Seigneur te donne pour que tu y demeures, tu entends dire par des gens:
In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
13 Des hommes d'iniquité se sont élevés parmi nous, et ils ont égaré ceux qui habitent notre territoire, et ils ont dit: Allons, et servons des dieux qui vous sont inconnus,
cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
14 Tu examineras, tu interrogeras, tu feras de nombreuses enquêtes, et s'il est manifeste que ces hommes ont ainsi parlé, et que cette abomination a eu lieu parmi vous,
to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
15 Tu feras périr par le glaive tous ceux qui habitent cette contrée, et vous la déclarerez anathème, elle et tout ce qu'elle renferme.
dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
16 Et tu feras, sur le grand chemin, un monceau de toutes ses dépouilles, et tu livreras aux flammes, devant le Seigneur ton Dieu, la ville et ses dépouilles, et elle sera toujours inhabitée, et on ne la rebâtira plus.
Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
17 Et rien de ce qui aura été frappé d'anathème ne te restera dans la main, afin que la colère du Seigneur se détourne, qu'il ait pitié de toi, qu'il te fasse miséricorde, et qu'il te multiplie, comme il l'a promis à tes pères,
Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
18 Si tu es docile à la parole du Seigneur ton Dieu pour mettre en pratique les commandements que je 'intime aujourd'hui, et faire ce qui est bon et agréable devant le Seigneur ton Dieu.
domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.