< Daniel 9 >

1 En la première année du règne de Darius, fils d'Assuérus, de la race des Mèdes, qui régna sur l'empire des Chaldéens,
A shekara ta fari da mulkin Dariyus ɗan Zerzes (wanda yake Bamediye), wanda aka mai da shi sarki a masarautar Babiloniyawa
2 Moi, Daniel, je compris, au moyen des livres, le nombre des années que la parole du Seigneur avait fait connaître à Jérémie le prophète, sur le temps que devait durer la désolation de Jérusalem, et qui devait être de soixante-dix années.
a shekara ta farko ta mulkinsa, ni, Daniyel na gane daga cikin littattafai, bisa ga maganar Ubangiji da aka faɗa wa annabi Irmiya, cewa zaman Urushalima kango zai kai shekara saba’in.
3 Et je tournai mon visage vers le Seigneur mon Dieu, pour l'implorer et le prier, en jeûnant, et revêtu d'un cilice.
Sai na juya wurin Ubangiji Allah na roƙe shi ta wurin addu’a da koke-koke, cikin azumi, ina saye da tsummoki, na kuma zauna a cikin toka.
4 Et je fis ma prière au Seigneur mon Dieu, et je lui rendis gloire, et je dis: Seigneur, Dieu grand et admirable, qui gardez votre alliance, et réservez votre miséricorde en faveur de ceux qui vous aiment et observent vos commandements;
Na yi addu’a ga Ubangiji Allahna na furta laifina. “Ya Ubangiji, mai alfarma da kuma Allah mai banrazana, wanda yake cika alkawarinsa na ƙauna ga duk wanda ya ƙaunace shi ya kuma kiyaye dokokinsa,
5 Nous avons péché; nous avons commis l'injustice et l'iniquité; nous nous sommes retirés de vous; nous avons dévié de vos ordonnances et de vos jugements,
mun yi zunubi muka kuma yi ba daidai ba. Mu mugaye ne da kuma’yan tawaye; mun juya wa umarninka da shari’unka baya.
6 Et nous n'avons point écouté vos serviteurs les prophètes, qui, en votre nom, parlaient à nos rois, à nos princes, à nos pères et à tout le peuple de la terre.
Ba mu saurari bayinka annabawa ba, waɗanda suka yi magana a sunanka ga sarakunanmu da masu mulkinmu da iyayenmu, da kuma dukan mutanen ƙasa.
7 À vous, Seigneur, est la justice; à nous la honte au visage, comme aujourd'hui à tout homme de Juda, à tout habitant de Jérusalem, à tout Israël, soit près d'ici, soit au loin, en toute région où vous les avez dispersés à cause des prévarications qu'ils ont commises.
“Ubangiji, kai mai adalci ne, amma a yau kunya ta rufe mu, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima da na dukan Isra’ila, waɗanda suke kusa da kuma nesa, a dukan ƙasashen da ka warwatsa mu saboda rashin amincinmu a gare ka.
8 En vous, Seigneur, est notre justice; à nous la honte au visage, à nous, à nos rois, à nos princes et à nos pères; car nous avons tous péchés contre vous.
Ya Ubangiji, mu da sarakunanmu, da masu mulkinmu da iyayenmu kunya ta rufe mu saboda mun yi maka zunubi.
9 À vous, Seigneur notre Dieu, les miséricordes et le pardon; car nous nous sommes retirés de vous,
Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne, mai gafartawa ne kuma, ko da yake mun yi masa tawaye;
10 Et nous n'avons point écouté la voix du Seigneur notre Dieu, pour marcher dans les lois qu'il nous a données, face à face, par les mains de ses serviteurs les prophètes.
ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ba, ba mu kuma kiyaye shari’unsa da ya ba mu ta wuri bayinsa annabawa ba.
11 Tout Israël a transgressé votre loi; il s'est détourné tout entier, pour ne pas entendre votre parole. Et votre malédiction est tombée sur nous, ainsi que l'imprécation écrite dans la loi de Moise, serviteur de Dieu, parce que nous avons péché contre vous.
Dukan Isra’ila sun karya dokokinka suka kuma juya maka baya, sun ƙi yi maka biyayya. “Saboda haka la’anoni da rantsuwar hukunce-hukuncen da suke a rubuce a cikin Dokar Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.
12 Et Dieu a confirmé ses paroles prononcées contre nous et contre les juges qui nous jugeaient, et qui ont amené sur nous de si grands maux, que jamais rien sous le ciel n'advint comme ce qui est advenu à Jérusalem;
Ka cika kalmomin da ka yi a kanmu da kuma a kan masu mulkinmu ta wurin kawo mana babban bala’i. A duniya duka ba a taɓa yin wani abu kamar yadda aka yi wa Urushalima ba.
13 Comme il est écrit en la loi de Moïse: Tous ces maux sont arrivés sur nous, et nous n'avons point prié devant la face du Seigneur notre Dieu, pour qu'il nous retirât de nos iniquités, et nous fit comprendre toute sa vérité.
Kamar yadda yake a rubuce cikin Dokar Musa, dukan wannan bala’i ya sauko a kanmu, duk da haka ba mu nemi tagomashin Ubangiji Allahnmu ta wurin barin aikatawa zunubanmu, mu kuma mai da hankali a kan gaskiyarka ba.
14 Mais le Seigneur a veillé sur nous, et il a amené sur nous ces maux, parce que le Seigneur notre Dieu est juste en toutes ses œuvres, et que nous n'avions point écouté sa voix.
Ubangiji bai yi wata-wata wajen kawo mana bala’i ba, domin Ubangiji Allahnmu mai adalci ne a cikin dukan abin da yake yi; duk da haka ba mu yi masa biyayya ba.
15 Et maintenant, Seigneur notre Dieu, qui par votre main puissante avez délivré votre peuple de la terre d'Égypte, et qui vous êtes fait alors un nom comme aujourd'hui, nous avons péché, nous avons commis l'iniquité!
“Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, wanda ya fito da mutanensa daga Masar ta hannu mai ƙarfi wanda kuma ya yi wa kansa sunan da ya dawwama har yă zuwa yau, mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba.
16 Seigneur, votre miséricorde est pour tous; que votre indignation et votre colère se détourne de votre ville de Jérusalem et de votre montagne sainte; car nous avons péché, et à cause de nos iniquités et de celles de nos pères, Jérusalem et votre peuple sont devenus un sujet d'opprobre pour tous ceux qui nous entourent.
Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
17 Et maintenant, Seigneur notre Dieu, écoutez la prière de votre serviteur et ses supplications; faites briller votre face dans votre sanctuaire délaissé; faites-le pour vous, Seigneur!
“Yanzu, ya Allahnmu, ka ji addu’o’i da koke-koken bayinka. Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka duba da rahama wurinka mai tsarki da ya zama kango.
18 Inclinez votre oreille, Seigneur mon Dieu, et exaucez-nous; ouvrez les yeux, et voyez notre anéantissement et celui de la cité à laquelle était donné votre nom; car ce n'est point dans l'attente de vos jugements que nous jetons devant vous notre cri de pitié, mais en vue de vos abondantes miséricordes, O Seigneur.
Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
19 Exaucez-moi, Seigneur; apaisez-vous, Seigneur; aimez-moi, Seigneur: ne différez pas, ô mon Dieu, pour l'amour de vous-même; car cette cité et ce peuple sont ceux à qui a été donné votre nom.
Ya Ubangiji, ka saurara! Ya Ubangiji ka gafarta! Ya Ubangiji, ka ji ka kuma yi wani abu! Saboda sunanka, ya Allahna, kada ka yi jinkiri, domin da sunanka ake kiran birninka da jama’arka.”
20 Et comme je parlais encore, comme je priais, et que je confessais mes péchés et les péchés d'Israël, mon peuple; comme je jetais en face du Seigneur mon Dieu mon cri de pitié pour la montagne sainte;
Yayinda da nake magana da addu’a, ina furta zunubina da zunubin mutanena Isra’ila ina miƙa koke-kokena ga Ubangiji Allahna saboda tudunsa mai tsarki,
21 Tandis que je parlais encore, voilà que l'homme Gabriel, qui m'était apparu au commencement de ma vision, vint en volant, et me toucha vers l'heure du sacrifice du soir.
yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
22 Et il m'ouvrit l'intelligence, et il me parla et me dit: Daniel, je suis venu pour t'apporter l'intelligence.
Ya umarce ni ya kuma ce mini, “Daniyel, yanzu na zo domin in ba ka hikima da ganewa.
23 Au commencement de ta prière, un ordre m'est venu, et je suis venu pour t'instruire; car tu es l'homme des désirs, dit-il. Réfléchis donc à ma parole et comprends ta vision.
Da zarar ka fara addu’a, an amsa, wadda na zo in faɗa maka, gama ana ƙaunar ka sosai. Saboda haka, ka yi lura da saƙon ka kuma fahimci wahayin.
24 Soixante-dix semaines ont été assignées à ton peuple et à la cité sainte, pour que le péché soit à sa fin, que les péchés soient abolis, que les iniquités soient effacées et expiées, que l'éternelle justice soit ramenée, que le sceau soit mis à la vision et au prophète, et que le Saint des saints soit marqué de l'onction.
“An ƙayyade wa jama’arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa’in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa’an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake haikali.
25 Sache donc et comprends qu'à partir de l'ordre qui sera donné de parler et de rebâtir Jérusalem, jusqu'au roi Christ, il y aura sept semaines et soixante-deux semaines; et l'ancien temps reviendra, les places et les remparts seront relevés, et les temps accomplis.
“Sai ka sani ka kuma fahimci wannan; Tun daga sa’ad da aka kafa doka don a maido a kuma sāke gina Urushalima har sai Shafaffen nan, mai mulki, ya zo, za a yi shekara arba’in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da mafaka.
26 Et après les soixante-deux semaines le Christ sera mis à mort, et il n'y aura pas en lui de sujet de condamnation; et il détruira la ville et le sanctuaire, à l'aide d'un chef qui surviendra; et ils disparaîtront dans un cataclysme, et à la fin de la guerre, qui sera abrégée, il livrera la ville aux désolations.
Bayan shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, za a datse Shafaffen nan zai kuma kasance ba shi da kome. Mutanen mai mulkin za su zo su hallaka birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen zai zo kamar rigyawa. Yaƙi zai ci gaba har ƙarshe, a kuma hallakar kamar yadda aka ƙaddara.
27 Et durant une semaine il confirmera l'alliance avec plusieurs. Et au milieu de la semaine la victime et les libations me seront ôtées, et l'abomination de la désolation sera sur le temple, et la désolation aura sa fin à la consommation des temps.
Zai tabbatar da alkawari da mutane masu yawa har na shekara bakwai. A tsakiyar bakwai ɗin nan ɗaya zai kawo ƙarshen duk wata hadaya da baiko. Kuma a kusurwar haikali zai sa abin ƙyama mai kawo hallaka, har sai ƙarshen da aka ƙaddara ya auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”

< Daniel 9 >