< Amos 9 >

1 J'ai vu le Seigneur debout sur l'autel, et Il a dit: Frappe sur le propitiatoire, et le temple sera ébranlé; frappe ensuite sur toutes les têtes. Et ceux qui resteront, Je les ferai périr par le glaive; nul n'échappera par la fuite, nul ne sera sauvé, ni ne trouvera de salut.
Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
2 Dussent-ils se cacher en enfer, Ma main les en arracherait; dussent-ils monter aux cieux, Je les en précipiterais. (Sheol h7585)
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
3 Dussent-ils s'enfermer dans les grottes du Carmel, je saurai les y trouver et les prendre; dussent-ils, hors de Ma vue, plonger dans les abîmes de la mer, Je donnerais Mes ordres au dragon, et il les suivrait.
Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
4 Dussent-ils partir captifs devant leurs ennemis, là Je commanderais au glaive, et il les exterminerait tous. Et J'attacherai sur eux Mes regards pour leur malheur, et non pour leur bien.
Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
5 Et le Seigneur Maître, Dieu tout-puissant, touche la terre, et elle est ébranlée; et tous ceux qui l'habitent seront dans la douleur; et la destruction montera comme le fleuve de l'Égypte, et descendra comme lui.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
6 C'est Lui qui bâtit des degrés pour monter au ciel, et affermit Sa promesse sur les fondements de la terre; c'est Lui qui appelle les eaux de la mer, et les verse sur la face de la terre; le Seigneur tout-puissant est Son Nom.
shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
7 Fils d'Israël, n'êtes-vous point pour Moi comme les fils des Éthiopiens? dit le Seigneur. N'est-ce point Moi qui ai fait venir Israël de l'Égypte, comme les Philistins de la Cappadoce, et les Syriens de la mer?
“Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
8 Voilà que le Seigneur Dieu a les yeux sur le royaume des pécheurs, et je l'effacerai de la terre. Mais Je n'enlèverai pas entièrement la maison de Jacob, dit le Seigneur.
“Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
9 Car c'est Moi qui commande, et je vannerai, parmi toutes les nations, la maison d'Israël, comme on vanne le blé au van, et pas un débris ne tombera par terre.
“Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
10 Tous les pécheurs de Mon peuple périront par le glaive, eux qui disent: Le malheur ne nous approchera pas, il ne viendra pas sur nous.
Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
11 Et ce jour-là Je relèverai le tabernacle de David, qui était tombé; J'en réparerai les brèches, J'en réédifierai les ruines, et Je le restaurerai comme il était dans les anciens jours,
“A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
12 afin que le reste des hommes et tous les gentils, par qui Mon Nom a été invoqué, Me cherchent, dit le Seigneur, qui fera toutes ces choses.
domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
13 Voilà que les jours arrivent, dit le Seigneur, où la moisson atteindra la vendange, et où la grappe noircira pendant les semailles. Et les montagnes ruisselleront de douceur, et toutes les collines seront plantées.
“Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
14 Et Je ramènerai Mon peuple Israël de la captivité, et ils réédifieront les villes détruites, et ils les habiteront; ils planteront des vignes, et ils en boiront le vin; ils cultiveront des jardins, et ils en mangeront les fruits.
Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
15 Et Je les rétablirai dans leur héritage, et ils ne seront plus arrachés de la terre que Je leur ai donnée, dit le Seigneur Dieu tout-puissant.
Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.

< Amos 9 >