< Amos 3 >

1 Écoutez cette parole qu'a dite le Seigneur contre vous, ô maison d'Israël, et contre toute ta famille que J'ai ramené de la terre d'Égypte, disant:
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 Hormis vous, Je n'ai connu aucune des tribus de la terre; et, à cause de cela, Je tirerai vengeance de vos péchés contre vous.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Deux hommes peuvent-ils marcher d'accord en toutes choses, s'ils ne se connaissent l'un l'autre?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Le lion rugira-t-il en sa forêt, s'il n'a quelque proie? Le lionceau donnera-t-il de la voix en son antre, s'il n'a rien ravi?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 L'oiseau tombera-t-il à terre sans oiseleur? Détendra-t-on le filet avant qu'il ait rien pris?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Sonnera-t-on de la trompette dans la ville sans que le peuple tremble, et y surviendra-t-il calamité qui ne soit envoyée par le Seigneur.
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Or le Seigneur ne fera rien qu'Il n'ait révélé Ses instructions à Ses serviteurs les prophètes.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 Le lion rugira, et qui n'en sera pas épouvanté? Le Seigneur Dieu a parlé: qui ne prophétisera point?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Faites des proclamations dans les villes des Assyriens, et dans les villes d'Égypte, et dites: Réunissez-vous en la montagne de Samarie, et voyez toutes les choses étranges qui se font au milieu d'elles, et l'oppression qui est en elles.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 Elle n'a point connu ce qui allait arriver contre ses habitants, et ils thésaurisent en leurs maisons l'iniquité et la misère.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Autour de toi, Tyr, on fera de ton territoire un désert; et ta puissance t'échappera, et tes champs seront dévastés.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Voici ce que dit le Seigneur: Tels, par le berger, sont arrachés de la gueule du lion deux jambes ou un lambeau d'oreille; tels seront arrachés les fils d'Israël qui demeureront en Samarie en face de la tribu du Jacob, et emmenés à Damas.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Prêtres, écoutez, et portez votre témoignage en la maison de Jacob, dit le Seigneur tout-puissant
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Le jour où Je punirai sur lui-même les impiétés d'Israël, je tirerai vengeance des autels de Béthel. Et les cornes de l'autel seront abattues et tomberont à terre.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Je renverserai et Je foulerai aux pieds la maison entourée de colonnes sur la maison d'été; et les maisons d'ivoire périront, et bien d'autres maisons seront enveloppées dans leur ruine, dit le Seigneur.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Amos 3 >