< 2 Samuel 22 >
1 Et David chanta ce cantique au Seigneur, le jour où le Seigneur l'eut délivré de Saül et de tous ses ennemis.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 Et il dit, en ce cantique: Seigneur, mon rocher, ma forteresse, mon sauveur!
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 Mon Dieu sera mon gardien, je me confierai à lui; mon protecteur, mon salut, mon refuge, vous me sauverez de l'homme inique.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 J'invoquerai le Seigneur, à qui appartient la louange, et il me délivrera de mes ennemis.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 Car les brisements de la mort m'ont investi, les torrents de l'iniquité m'ont frappé d'épouvante.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 Les angoisses de la mort m'ont entouré, l'agonie de la mort a pris l'avance sur moi. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
7 Dans mes afflictions j'invoquerai le Seigneur, je crierai à mon Dieu; de son temple, il entendra ma voix, mes cris arriveront à ses oreilles.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 La terre a été troublée, et elle a tremblé; les fondements du ciel ont été bouleversés, et ils se sont déchirés, parce que la colère du Seigneur a éclaté contre la terre et le ciel.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Dans sa fureur une fumée s'exhale, le feu de sa bouche est dévorant; des charbons en ont été embrasés.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 Il a abaissé les cieux et il est descendu, et les ténèbres s'étendaient sous ses pieds.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 Et il s'est assis sur les chérubins, et il a pris son essor, et il s'est montré sur les ailes des vents,
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 Et il s'est voilé de ténèbres. Et autour de lui, comme un tabernacle, il a étendu l'obscurité des eaux, condensées dans les nuées de l'air.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 Et les lueurs qui le précédaient ont mis des charbons en feu.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 Le Seigneur a tonné du haut du ciel, le très Haut a fait retentir sa voix.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 Il a lancé des traits et il a dispersé mes ennemis; il a fait tomber la foudre et il les a mis hors d'eux-mêmes.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 Aux reproches du Seigneur, sous le souffle de sa colère, on a vu les gouffres de la mer, et les bases de la terre ont apparu.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 Et il a envoyé d'en haut son ange, et il m'a pris, et il m'a tiré du tumulte des eaux.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 Il m'a délivré de la force de mes ennemis, de ceux qui me haïssaient et qui l'emportaient sur moi.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 Les jours de mon affliction s'étaient précipités sur moi; mais le Seigneur a été mon appui;
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 Il m'a conduit dans de libres espaces, et il m'a affranchi, parce qu'il se complaisait en moi.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 Le Seigneur m'a rétribué selon ma justice; il m'a rétribué selon la pureté de mes mains.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 Parce que j'ai suivi les voies du Seigneur, et que je n'ai point outragé mon Dieu.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 Parce que ses jugements et ses justices ont toujours été devant moi, et que je ne m'en suis jamais écarté.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 Je serai sans tache à ses yeux, et je me tiendrai en garde contre mes dérèglements.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Le Seigneur me rétribuera selon ma justice, et selon la pureté de mes mains devant ses yeux.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 Avec le saint vous serez saint, avec l'homme accompli vous serez accompli.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 Avec l'excellent vous serez excellent, avec le méchant vous serez méchant.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 Vous sauverez le peuple pauvre, et vous ferez baisser les yeux des superbes.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 Car, ô Seigneur, vous êtes ma lumière, et le Seigneur brillera devant moi dans mes ténèbres.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 Avec votre aide je courrai comme un homme fort; avec l'aide de mon Dieu je franchirai des remparts.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 Le Tout-Puissant, ses voies sont irréprochables; la parole du Seigneur est forte, éprouvée par le feu. Le Seigneur abrite tous ceux qui ont foi en lui.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 Qui donc est fort, hormis le Seigneur? Qui donc sera créateur, hormis notre Dieu?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 Le Tout-Puissant, c'est lui qui me fortifie par sa puissance, et qui m'a préparé une voie irréprochable.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Il rendu mes pieds légers comme ceux des cerfs; il m'a placé sur les hauts lieux.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 Vous avez exercé mes mains aux combats; vous avez brisé par mon bras un arc d'airain.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Vous m'avez donné, Seigneur, le bouclier qui me sauve; mon obéissance à vos ordres m'a grandi.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 L'espace sous mes pas s'est étendu, et mes jambes ont conservé leur fermeté.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 Je poursuivrai mes ennemis, et je les effacerai, et je ne reviendrai point qu'ils ne soient anéantis.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 Je les briserai, et ils ne se relèveront point; ils tomberont sous mes pieds.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Et vous, par votre puissance, vous me fortifierez, Seigneur, pendant la bataille, et vous courberez sous moi ceux qui contre moi se sont levés.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 Vous m'avez fait voir le dos de mes ennemis, vous avez mis à mort ceux qui me haïssaient.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 Ils n'ont plus de secours; ils crieront au Seigneur, mais le Seigneur ne les exaucera plus.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Je les ai broyés comme de la poussière; je les ai aplatis comme la boue du chemin.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Vous me préserverez, ô Seigneur, des contradictions des peuples; et vous me maintiendrez à la tête des nations; un peuple que je ne connaissais pas m'a été asservi;
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Les fils des étrangers m'avaient trompé; ils ont ouï votre parole, et ils m'ont été dociles.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Les fils des étrangers seront rejetés avec mépris, et ils trébucheront dans leurs places de retraite.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 Vive le Seigneur! béni soit mon gardien, et Dieu, le gardien de mon salut, sera glorifié.
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 Le Seigneur qui m'a vengé, en châtiant par mon bras les nations, est tout-puissant.
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 Il m'a tiré de leurs mains; vous m'élèverez encore, ô Seigneur, au- dessus de ceux qui se lèveront contre moi, vous me défendrez contre les hommes violents.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 A cause de cela, Seigneur, je vous rendrai gloire parmi toutes les nations, et je chanterai votre nom,
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 O vous, qui rendez grand le salut de votre roi, qui êtes miséricordieux envers David, votre christ, et envers sa postérité à jamais!
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”