< 2 Samuel 19 >
1 Or, des gens le rapportèrent à Joab, disant: Voilà que le roi pleure et se lamente à cause d'Absalon.
Aka faɗa wa Yowab cewa, “Sarki yana kuka, yana kuma makoki saboda Absalom.”
2 La victoire de ce jour s'est changée en deuil pour tout le peuple, parce que le peuple a ouï que le roi s'affligeait à cause de son fils.
Saboda haka sai nasarar da aka yi a ranar ta zama makoki ga dukan sojoji, gama a ranar, rundunoni sun ji an ce, “Sarki yana baƙin ciki domin ɗansa.”
3 Et l'armée se glissa en cachette dans la ville, comme s'y glisse une armée honteuse d'avoir pris la fuite pendant le combat.
Mutane fa suka shiga birni shiru, sai ka ce waɗanda sukan sace jiki don kunya sa’ad da suka gudo daga yaƙi.
4 Et le roi se voila la face, et le roi s'écria à haute voix, disant: Absalon, mon fils! Absalon, mon fils!
Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da ƙarfi yana cewa, “Ya ɗana Absalom! Ya Absalom ɗana, ɗana!”
5 Enfin, Joab entra auprès du roi en sa demeure, et il dit: Tu outrages tous les serviteurs qui aujourd'hui ont pris parti pour toi, et pour la vie de tes fils, de tes filles, de tes femmes et de tes concubines.
Sai Yowab ya shiga gidan sarki ya ce, “Yau ka kunyatar da dukan mutanenka, waɗanda ba da daɗewa ba sun ceci ranka, da rayukan’ya’yanka maza, da na’ya’yanka mata, da na matanka da kuma na ƙwarƙwaranka.
6 Puisque tu aimes ceux qui te haïssent et que tu hais ceux qui t'aiment, tu fais connaître que tes princes et tes serviteurs ne te sont rien; car je sais à présent que si Absalon était vivant, et nous tous morts, à tes yeux ce serait bien.
Kana ƙaunar maƙiyinka, kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Ka bayyana a fili cewa komandodi da sojojinsu ba kome ba ne a gare ka. Na ga cewa da za ka yi farin ciki, da a ce Absalom yana da rai a yau, dukanmu kuma mun mutu.
7 Lève-toi, sors, parle au cœur de tes serviteurs; car, je te jure par le Seigneur que si tu ne te mets en marche aujourd'hui, pas un homme ne passera cette nuit auprès de toi. Reconnais-le en toi-même: ce serait pour toi un malheur plus grand que tous ceux qui le sont venus, depuis ta première jeunesse jusqu'à cette heure.
Yanzu ka fita ka ƙarfafa mutanenka. Na rantse da Ubangiji, in ba ka fita ba, babu mutum guda da za a bari tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni fiye da kowace irin masifar da ta auko maka tun ƙuruciyarka har zuwa yanzu.”
8 Alors, le roi se leva, s'assit sur la porte, et toute l'armée se dit: Voilà le roi assis sur la porte. Et toute l'armée s'approcha du roi devant la porte; car Israël s'était enfui chacun sous sa tente.
Saboda haka sarki ya tashi, ya zauna a bakin hanyar shiga. Da aka faɗa wa mutane cewa, “Sarki yana zaune a bakin hanyar shiga,” sai duk suka zo gabansa. Ana cikin haka, Isra’ilawa dai sun riga sun tsere zuwa gidajensu.
9 Et le peuple de toutes les tribus d'Israël se mit à discuter, disant: Le roi David nous a délivrés de tous nos ennemis; c'est lui qui nous a affranchis du joug des Philistins, et il vient de s'enfuir de sa terre, de son royaume, à cause d'Absalon!
Mutane ko’ina a kabilan Isra’ila, suka yi ta gardama da juna, suna cewa, “Sarki ne ya cece mu daga hannun abokan gābanmu, shi ne kuma ya kuɓutar da mu daga hannun Filistiyawa. Amma ga shi ya tsere daga ƙasar saboda Absalom;
10 Cet Absalon que nous avions sacré, pour qu'il régnât sur nous, a été tué dans la bataille; pourquoi donc ne parlez-vous pas de rappeler David? Or, les discours de tout Israël arrivèrent jusqu'au roi.
kuma shi Absalom, da muka naɗa yă yi mulkinmu, ya mutu a yaƙi. Saboda haka don me ba kwa ce wani abu game da dawo da sarki?”
11 Et le roi David envoya auprès des prêtres Sadoc et Abiathar, disant: Parlez aux anciens de Juda, dites-leur: Pourquoi donc êtes-vous les derniers à rappeler le roi en sa demeure? Les discours de tout Israël sont arrivés jusqu'au roi, au lieu où il réside.
Sai Sarki Dawuda ya aika da saƙo zuwa wurin Zadok da Abiyatar, firistoci, ya ce, “Ku tambayi dattawan Yahuda, ‘Me ya sa ku ne za ku zama na ƙarshe a yin tunanin komar da sarki zuwa fada, da yake abin da ake faɗi ko’ina a Isra’ila ya kai kunnen sarki a mazauninsa?
12 Vous êtes mes frères, vous êtes ma chair et mes os: pourquoi donc êtes- vous les derniers à ramener le roi dans sa demeure?
Ku’yan’uwana ne, jikina, jinina kuma. To, don me za ku zama na ƙarshe na yarda a dawo da sarki zuwa fada?’
13 Et vous direz à Amessaï: David dit: N'es-tu pas ma chair et mes os? Que le Seigneur me punisse et qu'il me punisse encore, si tu ne deviens pas, devant moi pour toujours, le général en chef de toutes nos armées, à la place de Joab.
Ku kuma ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba jikina ba ne da jinina? Allah yă hukunta ni, da hukunci mai tsanani, idan daga yanzu ba ka zama komandan sojojina a maimakon Yowab ba.’”
14 Il gagna ainsi le cœur de tous les hommes de Juda, comme le cœur d'un seul homme; et ils envoyèrent au roi, et ils lui dirent: Reviens avec tous tes serviteurs.
Ta haka ya rinjayi zukatan dukan mutane Yahuda, kamar mutum ɗaya. Suka aika da saƙo wurin sarki suka ce, “Ka dawo, kai da dukan mutanenka.”
15 Et le roi se mit en marche; il alla jusqu'au Jourdain, et tous les hommes de Juda se portèrent à sa rencontre à Galgala, pour le ramener en deçà du fleuve.
Sa’an nan sarki ya dawo, ya kuma tafi har zuwa Urdun. To, mutanen Yahuda suka zo Gilgal don su fita su taryi sarki, su kuma kawo shi ƙetaren Urdun.
16 Et Seméï, fils de Géra, de la famille de Jémini en Bathurim, se hâta, et il se mêla aux hommes de Juda, pour aller au-devant du roi David.
Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuda don su taryi Sarki Dawuda.
17 Il avait avec lui mille hommes de Benjamin, et Siba le serviteur de Saül, et ses quinze fils, et ses vingt serviteurs; ils marchèrent droit au Jourdain, au-devant du roi.
Tare da shi akwai kabilar Benyamin mutum dubu, tare da Ziba, mai hidimar gidan Shawulu, da’ya’yansa maza goma sha biyar, da bayi ashirin. Suka ruga zuwa Urdun, inda sarki yake.
18 Et ils préparèrent le service du passage du roi; ils lui menèrent un bac pour exciter l'ardeur de la maison du roi, et pour qu'il fût fait selon le bon plaisir de David. Or, Seméï, fils de Géra, se jeta devant lui la face contre terre, dès qu'il eut passé le Jourdain.
Suka haye a mashigin don su ƙetaro da iyalin sarki, su kuma yi duk abin da yake so. Sa’ad da Shimeyi ɗan Gera ya haye Urdun, sai ya fāɗi rubda ciki a gaban sarki
19 Et il dit au roi: Que mon Seigneur ne tienne pas compte de mon iniquité, qu'il ne se souvienne pas que son serviteur a péché le jour où mon seigneur est sorti de Jérusalem; puisse-t-il ne l'avoir point à cœur!
ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka riƙe laifina a zuciya. Kada ka tuna da laifin da na yi maka ranka yă daɗe, ranan nan da kake gudu daga Urushalima. Kada ka tuna da shi ko kaɗan.
20 Car ton serviteur a reconnu sa faute, et voilà que j'arrive aujourd'hui le premier de tout Israël et de la maison de Joseph, pour m'humilier devant le roi mon seigneur.
Na sani ni bawanka na yi maka laifi. Shi ya sa na zama na farko daga dukan Gidan Yusuf, da mutanen Isra’ila wanda ya fito don yă tarye ka yau, ranka yă daɗe, sarki.”
21 Abessa, fils de Sarvia, dit: Est-ce que Semeï ne sera pas mis à mort, pour avoir maudit l'oint du Seigneur?
Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce, “Bai kamata a kashe Shimeyi saboda wannan ba? Ya la’anci shafaffe na Ubangiji.”
22 Mais David dit: Qu'y a-t-il entre vous et moi, fils de Sarvia, pour qu'aujourd'hui vous me tendiez un piège? Nul homme en Israël aujourd'hui ne sera mis à mort; est-ce que j'ignore que je règne sur Israël?
Dawuda ya ce, “Me ya haɗa ni da ku, ku’ya’yan Zeruhiya? Yau ɗin nan kun zama maƙiyana! Ya kamata a kashe wani a Isra’ila a yau? Ban san cewa yau ni sarki ne a bisa Isra’ila ba?”
23 Et le roi dit à Sémeï: Tu ne mourras point; et il le lui jura.
Saboda haka sarki ya ce wa Shimeyi, “Ba za ka mutu ba.” Sarki kuwa ya yi alkawari har da rantsuwa.
24 Miphiboseth, petit-fils de Saül, alla aussi à la rencontre du roi; il n'avait pris aucun soin de ses pieds; il ne s'était point coupé les ongles, il ne s'était point rasé autour des lèvres, il n'avait point lavé ses vêtements, depuis le jour où le roi avait quitté Jérusalem jusqu'à ce jour où il revenait en paix.
Mefiboshet, jikan Shawulu, shi ma ya gangara don yă taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har ran da ya komo lafiya, Mefiboshet bai lura da ƙafafunsa, ko yă aske gemunsa, ko yă wanke tufafinsa ba.
25 Et lorsqu'il alla à la rencontre du roi retournant à Jérusalem, David lui dit: Pourquoi n'es-tu point venu avec moi, Miphiboseth?
Sa’ad da ya zo daga Urushalima don yă taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba Mefiboshet?”
26 Miphiboseth lui répondit: O roi mon seigneur, mon serviteur m'a trompé, car ton serviteur lui avait dit: bâte-moi l'ânesse, que je la monte, et je suivrai le roi (tu sais que ton serviteur est boiteux).
Sai ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, da yake bawanka gurgu ne, na ce, ‘A sa mini sirdi a kan jakina don in hau in tafi tare da sarki.’ Amma Ziba bawana ya bashe ni.
27 Or, Siba a usé d'artifice à l'égard de ton serviteur, devant le roi mon seigneur. Le roi mon seigneur est comme un ange de Dieu, qu'il fasse de moi ce que bon lui semble.
Ya kuwa ɓata suna bawanka a gaban ranka yă daɗe, sarki. Ranka yă daɗe, sarki yana kama da mala’ikan Allah, ka yi abin da ka ga ya fi maka kyau.
28 Car tous ceux de la maison de mon père étaient des hommes de mort, devant le roi mon seigneur, quand tu as fait de ton serviteur l'un de tes convives. Quelle justification peut donc m'être permise pour que je crie encore devant le roi?
Duk zuriyar kakana ba su cancanci kome ba sai mutuwa daga ranka yă daɗe, amma ka ba wa bawanka wuri cikin mutanen da suke ci a teburinka. Saboda haka, wanda’yanci nake da shi da zan yi wani ƙarin roƙo a wurin sarki?”
29 Et le roi lui dit: Qu'est-il besoin que tu parles davantage? J'ai prononcé: Siba et toi vous partagerez les champs.
Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”
30 Miphiboseth reprit: Qu'il prenne tout, puisque le roi mon seigneur rentre en paix dans sa demeure.
Mefiboshet ya ce wa sarki, “Bari yă ɗauki kome, yanzu da ranka yă daɗe, sarki ya dawo gida lafiya.”
31 Or, Berzelli le Galaadite était sorti de Rhogellim, et il avait passé le Jourdain avec le roi, afin de l'escorter de l'autre côté du fleuve.
Barzillai mutumin Gileyad shi ma ya zo daga Rogelim don yă ƙetare Urdun tare da sarki, yă kuma sallame shi daga can.
32 Berzelli était un homme très âgé: il avait quatre-vingts ans; il avait nourri le roi pendant son séjour à Manaïm, car il était extrêmement riche.
To, Barzillai fa tsoho ne, mai shekara tamanin. Ya tanada wa sarki a lokaci da yake Mahanayim, gama shi attajiri ne.
33 Le roi lui dit: Tu vas venir plus loin avec moi, et je nourrirai, auprès de moi, ta vieillesse à Jérusalem.
Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka ƙetaro tare da ni ka zauna tare da ni a Urushalima, zan kuwa tanada maka.”
34 Mais Berzelli lui répondit: Combien de jours me reste-t-il à vivre, pour que j'aille avec le roi à Jérusalem?
Amma Barzillai ya ce wa sarki, “Shekara nawa ya rage mini har da zan tafi Urushalima da sarki?
35 J'ai aujourd'hui quatre-vingts ans; puis-je encore discerner le bon et le mauvais? Ton serviteur trouve-t-il quelque goût à ce qu'il mange et à ce qu'il boit? Écoute-t'il avec plaisir la voix des chanteurs et des chanteuses? Pourquoi ton serviteur irait-il attrister son seigneur et son roi?
Yanzu ina da shekara tamanin. Zan iya bambanta abu mai daɗi da marar daɗi kuma ne? Bawanka zai iya jin ɗanɗano abin da yake ci, ko yake sha ne? Har yanzu zan iya jin muryoyin mawaƙan maza da mata? Don me bawanka zai zama ƙari kaya ga ranka yă daɗe?
36 Ton serviteur accompagnera son roi quelque peu au delà du fleuve. Pourquoi donc le roi me donnerait-il une si grande récompense?
Bawanka zai ƙetare Urdun tare da sarki, yă ɗan yi maka rakiya kaɗan. Me ya sa ranka yă daɗe zai ba ni irin wannan lada.
37 Que ton serviteur reste en repos; je mourrai dans ma ville, auprès du sépulcre de mon père et de ma mère; voilà ton serviteur Chamaam, mon fils; il suivra plus loin le roi mon seigneur; traite-le comme bon te semblera.
Ka bar bawanka yă koma, don in mutu a garina, kusa da kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ga bawanka Kimham. Bari yă ƙetare tare da ranka yă daɗe, sarki. Ka yi abin da ka ga dama da shi.”
38 Le roi reprit: Que Chamaam vienne avec moi, et je le traiterai de mon mieux; et tout ce que tu pourras désirer de ma main, je le ferai pour toi.
Sarki ya ce, “Kimham zai ƙetare tare da ni, zan kuwa yi masa abin da ya gamshe ka. Kuma duk abin da kake bukata a wurina, zan yi maka.”
39 Et l'armée entière franchit le Jourdain, le roi passa; puis, il baisa Berzelli et le bénit, et celui-ci retourna en sa demeure.
Saboda haka dukan mutane suka ƙetare Urdun, sa’an nan kuma sarki ma ya ƙetare. Sarki ya yi wa Barzillai sumba ya albarkace shi, sa’an nan Barzillai ya koma gidansa.
40 Le roi se rendit ensuite à Galgala, et Chamaam le suivit; il y avait avec le roi tout le peuple de Juda et la moitié d'Israël.
Sa’ad da sarki ya ƙetare zuwa Gilgal, Kimham ma ya ƙetare tare da shi. Dukan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra’ila suka ƙetare da sarki.
41 Et tous ceux d'Israël allèrent trouver le roi, et ils lui dirent: Pourquoi nos frères de Juda nous ont-ils dérobé le roi? Pourquoi l'ont-ils escorté quand il a traversé le fleuve avec toute sa maison et tous les hommes de sa suite?
Nan take sai ga mutane Isra’ila suna zuwa wurin sarki, suna cewa, “Don me’yan’uwanmu, mutanen Yahuda, suka saci sarki, suka kawo shi da iyalinsa a ƙetaren Urdun, tare da dukan mutanensa?”
42 Ceux de Juda répondirent à ceux d'Israël, et ils dirent: Pourquoi le roi nous est-il proche? et pourquoi à ce sujet vous irritez-vous si fort? Avons- nous mangé aux dépens du roi? nous a-t-il fait des présents? a-t-il levé quelque tribut pour nous?
Dukan mutanen Yahuda suka ce wa mutanen Isra’ila, “Mun yi haka domin sarki danginmu na kurkusa ne. Don me kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abu daga cikin kayan sarki ne? Mun ɗauki wani abu wa kanmu ne?”
43 Et ceux d'Israël répliquèrent: Nous avons dix bras au service du roi, nous sommes vos premiers-nés, nous sommes plus que vous auprès de David. Pourquoi donc nous injurier et ne pas tenir compte de ce qu'avant Juda nous avons parlé de ramener notre roi? Or, les paroles de ceux de Juda avaient été plus dures que celles d'Israël.
Sa’an nan mutanen Isra’ila suka ce wa mutanen Yahuda, “Muna da rabo goma a wurin sarki; ban da haka ma, muna da hakki mafi yawa a wurin Dawuda fiye da ku. Don me kuke mana reni? Ba mu ne ma muka fara magana dawowa da sarki ba?” Amma mutanen Yahuda suka ɗauka maganar da zafi fiye da mutanen Isra’ila.